< Mahukunta 7 >
1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
Und Jerubbaal, das ist Gideon, stand früh auf und alles Volk, das mit ihm war, und sie lagerten an der Quelle Charod, und das Lager Midjans war ihm gegen Mitternacht am Hügel Moreh im Talgrunde.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
Und Jehovah sprach zu Gideon: Zu viel ist das Volk mit dir, als daß Ich Midjan in ihre Hand geben könnte, auf daß Israel nicht prahle über Mich und spreche: Meine Hand hat mich gerettet.
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
Und rufe nun aus vor den Ohren des Volkes und sage: Wer sich fürchtet und erzittert, der kehre zurück und hebe sich hinweg vom Gebirge Gilead. Und es kehrten vom Volke zurück zweiundzwanzigtausend, und zehntausend verblieben.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
Und Jehovah sprach zu Gideon: Noch ist des Volkes zu viel. Bringe sie hinab an das Wasser. Daselbst will Ich sie läutern; und soll sein, von wem Ich dir sagen werde, dieser soll mit dir ziehen, der soll mit dir ziehen; und jeder, von dem Ich dir sage, dieser soll nicht mit dir ziehen, der ziehe nicht.
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
Und er brachte das Volk hinab an das Wasser, und Jehovah sprach zu Gideon: Jeder, der vom Wasser mit der Zunge leckt, wie der Hund leckt, den stelle besonders, und auch jeden, der auf die Knie niederkauert, um zu trinken.
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
Und es war die Zahl derer, die mit der Hand zum Munde geleckt hatten, dreihundert Mann; und alles übrige Volk kauerte auf die Knie nieder, um Wasser zu trinken.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
Und Jehovah sprach zu Gideon: Mit den dreihundert Mann, die geleckt haben, rette Ich euch und gebe Midjan in deine Hand; und all das Volk laß jeden Mann an seinen Ort gehen.
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
Und sie nahmen Zehrung für das Volk in ihre Hand, und ihre Posaunen, und alle Männer Israels entließ er, jeden Mann in sein Zelt, und die dreihundert Mann hielt er zurück. Und das Lager Midjans war unter ihnen im Talgrunde.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
Und es geschah in selbiger Nacht, daß Jehovah zu ihm sprach: Mache dich auf und gehe hinab in das Lager, denn Ich habe es in deine Hand gegeben.
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
Fürchtest du dich aber, hinabzugehen, so gehe du und dein Junge Purah hinab zum Lager.
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
Und du wirst hören, was sie reden, und danach werden deine Hände stark werden, daß du in das Lager hinabgehst. Und er ging hinab, er und Purah, sein Junge, an das Ende der Kampfgerüsteten im Lager.
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
Und Midjan und Amalek und alle Söhne des Ostens lagen im Talgrunde, wie die Heuschrecke an Menge, und ihrer Kamele war keine Zahl, wie der Sand am Strande des Meeres an Menge.
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
Und Gideon kam und siehe, ein Mann erzählte seinem Genossen einen Traum und sprach: Siehe, ich träumte einen Traum, und siehe, ein geröstet Gerstenbrot rollte in das Lager Midjans und kam an das Zelt und schlug dasselbe, daß es fiel, und kehrte es zuoberst, und das Zelt war gefallen.
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
Und sein Genosse antwortete und sprach: Dies ist nichts anderes, als das Schwert Gideons, des Sohnes von Joasch, des Mannes von Israel. Gott hat Midjan und das ganze Lager in seine Hand gegeben.
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
Und es geschah, als Gideon den Traum erzählen und deuten hörte, so betete er an und kehrte in Israels Lager zurück und sprach. Machet euch auf, denn Jehovah hat das Lager Midjans in eure Hand gegeben.
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
Und er teilte die dreihundert Mann in drei Haufen und gab ihnen allen Posaunen in die Hand und leere Krüge und Fackeln inmitten der Krüge.
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
Und er sprach zu ihnen: Von mir sehet es ab und tuet also; und siehe, ich komme dahin an das Ende des Lagers, und es geschehe, daß wie ich tue, also sollt ihr tun.
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
Und stoße ich in die Posaune, ich und alle, die mit mir sind, so stoßet auch ihr rings um das ganze Lager in die Posaunen und sprechet: Für Jehovah und für Gideon!
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
Und es kam Gideon und die hundert Mann, die mit ihm waren, am Anfang der mittleren Nachtwache an das Ende des Lagers, da sie eben die Hut aufgestellt hatten, und stießen in die Posaunen und zerschmissen die Krüge in ihrer Hand.
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
Und es bliesen alle drei Haufen mit den Posaunen und zerbrachen die Krüge und hielten die Fackeln in der linken Hand und die Posaunen zum Blasen in der rechten Hand und riefen: Schwert für Jehovah und für Gideon!
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
Und sie standen, jeder Mann an seiner Stelle, rings um das Lager; und das ganze Lager rannte, und sie schrien und flohen.
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
Und die dreihundert bliesen die Posaunen, und Jehovah setzte im Lager das Schwert eines jeden Mannes wider seine Genossen und wider das ganze Lager; und das Lager floh bis Beth-Schittah, Zererath zu, bis an den Rand von Abel-Mecholah bei Tabbath.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
Und die Männer Israels wurden aufgerufen aus Naphthali und aus Ascher und aus ganz Menascheh, und sie setzten hinter Midjan nach.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
Und Gideon sandte Boten in das ganze Gebirge Ephraim und sprach: Gehet hinab, Midjan entgegen, und gewinnet die Wasser vor ihnen bis Beth-Barah und den Jordan; und jeder Mann in Ephraim wurde aufgerufen, und sie gewannen die Wasser bis Beth-Barah und den Jordan.
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
Und sie fingen zwei Oberste Midjans, Oreb und Seeb, und erwürgten Oreb auf Zur-Oreb und Seeb erwürgten sie in Jekeb-Seeb und sie setzten Midjan nach, und brachten die Köpfe Orebs und Seebs zu Gideon, jenseits des Jordan.