< Mahukunta 7 >

1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
Jérubbahal donc, qui [est] Gédeon, se levant dès le matin, et tout le peuple qui était avec lui, ils se campèrent près de la fontaine de Harod, et ils avaient le camp de Madian du côté du Septentrion, vers le coteau de Moreh dans la vallée.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
Or l'Eternel dit à Gédeon: Le peuple qui est avec toi est en trop grand nombre, pour que je livre Madian en leur main, de peur qu'Israël ne se glorifie contre moi, en disant: Ma main m'a délivré.
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
Maintenant donc fais publier, le peuple l'entendant, et qu'on dise: Quiconque est timide et a peur, qu'il s'en retourne, et s'en aille dès le matin du côté de la montagne de Galaad; et vingt-deux mille du peuple s'en retournèrent; et il en resta dix mille.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
Et l'Eternel dit à Gédeon: Il y a encore du peuple en trop grand nombre; fais-les descendre vers l'eau, et là je te les choisirai; et celui dont je te dirai, celui-ci ira avec toi, il ira avec toi; et celui duquel je te dirai, celui-ci n'ira point avec toi; il n'y ira point.
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
Il fit donc descendre le peuple vers l'eau; et l'Eternel dit à Gédeon: Quiconque lapera l'eau de sa langue, comme le chien lape, tu le mettras à part; et [tu mettras aussi à part] tous ceux qui se courberont sur leurs genoux pour boire.
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
Et le nombre de ceux qui lapaient l'eau dans leur main, [la] portant à leur bouche, fut de trois cents hommes; mais tout le reste du peuple se courba sur ses genoux, pour boire de l'eau.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
Alors l'Eternel dit à Gédeon: Je vous délivrerai par le moyen de ces trois cents hommes qui ont lapé [l'eau], et je livrerai Madian en ta main. Que tout le peuple donc s'en aille, chacun en son lieu.
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
Ainsi le peuple prit en sa main des provisions, et leurs trompettes. Et Gédeon renvoya tous les hommes d'Israël chacun en sa tente, et retint les trois cents hommes. Or le camp de Madian était au-dessous, dans la vallée.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
Et il arriva cette nuit-là, que l'Eternel lui dit: Lève-toi, descends au camp, car je l'ai livré en ta main.
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
Et si tu crains d'y descendre, descends vers le camp toi et Purah ton serviteur.
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
Et tu entendras ce qu'ils diront, et tes mains seront fortifiées, puis tu descendras au camp. Il descendit donc avec Purah son serviteur, jusqu'au premier corps de garde du camp.
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
Or Madian, et Hamalec, et tous les Orientaux, étaient répandus dans la vallée comme des sauterelles, tant il y en avait, et leurs chameaux étaient sans nombre, comme le sable qui est sur le bord de la mer, tant il y en avait.
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
Gédeon donc y étant arrivé, voilà, un homme récitait à son compagnon un songe, et lui disait: Voici, j'ai songé un songe; il me semblait qu'un gâteau de pain d'orge se roulait vers le camp de Madian, et qu'étant venu jusqu'aux tentes, il les a frappées, de sorte qu'elles en sont tombées, et il les a renversées, [en roulant] du haut [de la montagne], et elles sont tombées.
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
Alors son compagnon répondit, et dit: Cela n'est autre chose que l'épée de Gédeon, fils de Joas, homme d'Israël. Dieu a livré Madian et tout ce camp en sa main.
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
Et quand Gédeon eut entendu le récit du songe, et son interprétation, il se prosterna; et étant retourné au camp d'Israël, il dit: Levez-vous, car l'Eternel a livré le camp de Madian en vos mains.
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
Puis il divisa les trois cents hommes en trois bandes, et leur donna à chacun des trompettes à la main, et des cruches vides, et des flambeaux dans les cruches.
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
Et il leur dit: Prenez garde à moi et faites comme je ferai; lorsque je serai arrivé au bout du camp, vous ferez comme je ferai.
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
Quand donc je sonnerai de la trompette, et tous ceux aussi qui sont avec moi, alors vous sonnerez aussi des trompettes autour de tout le camp, et vous direz: L'EPEE DE L'ETERNEL, ET DE GEDEON.
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
Gédeon donc, et les cent hommes qui étaient avec lui, arrivèrent au bout du camp, comme on venait de poser la seconde garde; on ne faisait que poser les gardes lorsqu'ils sonnèrent des trompettes; et qu'ils cassèrent les cruches qu'ils avaient en leurs mains.
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
Ainsi les trois bandes sonnèrent des trompettes, et cassèrent les cruches, tenant en leur main gauche les flambeaux, et en leur main droite les trompettes pour sonner, et ils criaient: L'EPEE DE L'ETERNEL, ET DE GEDEON.
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
Et ils se tinrent chacun en sa place autour du camp; et toute l'armée courait ça et là, s'écriant et fuyant.
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
Car comme les trois cents hommes sonnaient des trompettes, l'Eternel tourna l'épée d'un chacun contre son compagnon, même par tout le camp. Et l'armée s'enfuit jusqu'à Beth-sittah, vers Tserera, jusqu'au bord d'Abelmeholah, vers Tabbat.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
Et les hommes d'Israël, [savoir] de Nephthali et d'Aser, et de tout Manassé s'assemblèrent, et poursuivirent Madian.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
Alors Gédeon envoya des messagers par toute la montagne d'Ephraïm, pour leur dire: Descendez pour aller à la rencontre de Madian, et saisissez-vous les premiers des eaux du Jourdain jusqu'à Beth-bara. Les hommes d'Ephraïm donc s'étant assemblés, se saisirent des eaux du Jourdain jusqu'à Beth-bara.
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
Et ils prirent deux des chefs de Madian, Horeb et Zééb, et ils tuèrent Horeb au rocher de Horeb; mais ils tuèrent Zééb au pressoir de Zééb; et ils poursuivirent Madian, et apportèrent les têtes de Horeb et de Zééb à Gédeon, au deçà du Jourdain.

< Mahukunta 7 >