< Mahukunta 7 >
1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
Then Jerubbaal, the same, is Gideon, and all the people that were with him, rose up early, and encamped by the fountain of Harod, —and, the camp of Midian, was on the north of them, by the hill of Moreh, in the vale.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
And Yahweh said unto Gideon, Too many, are the people that are with thee, for me to deliver the Midianites into their hand, —lest Israel vaunt themselves against me, saying, Mine own hand, hath saved me.
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
Now, therefore, proclaim, I pray thee, in the ears of the people, saying, Whoso feareth and trembleth—let him turn and go back from Mount Gilead. And there returned of the people twenty-two thousand, and, ten thousand, remained.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
Then said Yahweh unto Gideon—Yet, are the people too many, take them down unto the waters, that I may prove them for thee, there, —and it shall be, that, he of whom I say unto thee, This one, shall go with thee, the same, shall go with thee, and, every one of whom I say unto thee, This one, shall not go with thee, the same, shall not go.
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
So he took down the people unto the waters, —and Yahweh said unto Gideon—Every one that lappeth with his tongue of the water, as a dog lappeth, thou shalt set him by himself, likewise, every one that boweth down upon his knees, to drink.
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
And so it was, that, the number of them that lapped with their hand to their mouth, was three hundred men, —but, all the rest of the people, bowed down on their knees, to drink water.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
Then said Yahweh unto Gideon—By the three hundred men that lapped, will I save you, and deliver the Midianites into thy hand; and let, all [the rest of] the people, go every man to his own place.
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
So the people took provisions in their hand, and their horns, but, every man of Israel besides, sent he away every man to his home, whereas, the three hundred men, he retained. Now, the camp of Midian, was beneath him in the vale.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
And it came to pass, on that night, that Yahweh said unto him, Arise! go down against the camp, —for I have delivered it into thy hand.
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
Or, if, thou, art afraid to go down, go down—thou and Purah thy young man, unto the camp;
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
so shalt thou hear what they shall say, —and, afterward, shall thy hands grow strong, and thou shalt go down against the camp. Then went he down, he and Purah his young man, unto the outmost part of the armed men that were in the camp.
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
Now, the Midianites and the Amalekites and all the sons of the east, were lying along in the vale, like locusts for multitude, —their camels also, were without number, as the sand that is by the sea side, for multitude.
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
And Gideon came in, and lo! a man relating to his neighbour a dream, —and he said—Lo! a dream, have I dreamt, and lo! a round cake of barley bread tumbling into the camp of Midian, and it came as far as the tent—and smote it that it fell, and turned it upside down, and the tent lay along.
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
Then responded his neighbour and said: —Nothing else, is this, than the sword of Gideon son of Joash, a man of Israel, —God hath delivered into his hand, both Midian and all the host.
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
And it was so, when Gideon heard the story of the dream, and the interpretation thereof, that he bowed himself down, —and returned unto the camp of Israel, and said—Arise! for Yahweh hath delivered into your hand the host of Midian.
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
And he divided the three hundred men, into three companies, —and put horns into the hands of them all, with empty pitchers, and torches inside the pitchers.
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
Then he said unto them, On me, shall ye look, and, in like manner, shall ye do, —and lo! when I am coming unto the outermost part of the camp, then shall it be, that, as I do, so, shall ye do.
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
When I shall blow with the horn, I and all who are with me, then shall, ye also, round about all the camp, blow with your horns, and shall say, For Yahweh and for Gideon!
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
So Gideon came, and the hundred men that were with him, unto the outermost part of the camp, at the beginning of the middle watch, they had but, newly set, the watchers, —and they blew with the horns, and brake in pieces the pitchers, that were in their hand.
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
Yea the three companies blew with the horns, and shivered the pitchers, and caught hold—with their left hands—of the torches, while, in their right hands, were the horns, to blow with, —and they cried, A sword for Yahweh, and for Gideon!
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
And they stood still, every man in his place, round about the camp, —and all the host ran and shouted, and fled.
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
When the three hundred blew the horns, Yahweh set the sword of every man, against his neighbour, and against all the host, —and the host fled, as far as the Place of Acacias, towards Zererath, as far as the border of Abel-meholah, by Tabbath.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
And the men of Israel were called together, out of Naphtali and out of Asher, and out of all Manasseh, —and pursued Midian.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
And, messengers, did Gideon send through all the hill country of Ephraim, saying—Go down to meet Midian, and capture, before them, the waters, as far as Beth-barah, and the Jordan. So all the men of Ephraim were called out, and captured the waters, as far as Beth-barah, and the Jordan.
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
And they captured the two princes of Midian, Oreb and Zeeb, and slew Oreb at Oreb’s Rock, and, Zeeb, they slew at Zeeb’s Winepress, and pursued Midian, —and, the heads of Oreb and Zeeb, brought they in unto Gideon at the ford of the Jordan.