< Mahukunta 7 >
1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
And Jerubbaal, who is Gideon, arose early, and all the people that were with him, and they encamped beside the spring Harod; and he had the camp of Midian on the north by the hill of Moreh in the valley.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
And Jehovah said to Gideon, The people that are with thee are too many for me to give Midian into their hand, lest Israel vaunt themselves against me, saying, Mine own hand hath saved me.
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
And now proclaim in the ears of the people, saying, Whoever is timid and afraid, let him go back and turn from mount Gilead. And there went back of the people twenty-two thousand; and there remained ten thousand.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
And Jehovah said to Gideon, Still the people are many; bring them down to the water, and I will try them for thee there, and it shall be, that of whom I shall say unto thee, This shall go with thee, the same shall go with thee; and of whomsoever I shall say unto thee, This shall not go with thee, the same shall not go.
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
And he brought down the people to the water; and Jehovah said to Gideon, Every one that lappeth of the water with his tongue, as a dog lappeth, him shalt thou set by himself; likewise every one that boweth down on his knees to drink.
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
And the number of them that lapped, with their hand to their mouth, were three hundred men; and all the rest of the people bowed down on their knees to drink water.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
And Jehovah said to Gideon, By the three hundred men that lapped will I save you, and give Midian into thy hand; and let all the people go every man to his place.
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
And they took the victuals of the people in their hand, and their trumpets; and all the men of Israel he sent away, every man to his tent, but retained the three hundred men. Now the camp of Midian was beneath him in the valley.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
And it came to pass in that night, that Jehovah said to him, Arise, go down to the camp; for I have given it into thy hand.
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
And if thou fear to go down, go thou with Phurah thy servant down to the camp;
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
and thou shalt hear what they say; and afterwards shall thy hand be strengthened, and thou shalt go down unto the camp. And he went down with Phurah his servant to the outside of the armed men that were in the camp.
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
And Midian and Amalek and all the children of the east lay along in the valley as locusts for multitude; and their camels were without number, as the sand upon the sea-shore for multitude.
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
And Gideon came, and behold, a man was telling a dream to his fellow; and he said, Behold, I dreamed a dream, and lo, a cake of barley-bread tumbled into the camp of Midian, and came to the tent, and smote it that it fell, and overturned it; and the tent lay along.
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
And his fellow answered and said, This is nothing else save the sword of Gideon the son of Joash, the man of Israel: God hath given into his hand Midian and all the host.
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
And it came to pass when Gideon heard the telling of the dream and its interpretation, that he worshipped. And he returned into the camp of Israel, and said, Arise; for Jehovah hath given into your hand the camp of Midian.
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
And he divided the three hundred men into three companies, and he put a trumpet in every man's hand, and empty pitchers, and torches within the pitchers.
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
And he said to them, Look on me, and do likewise; behold, when I come to the extremity of the camp, it shall be that, as I do, so shall ye do.
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
And when I blow with a trumpet, I and all that are with me, ye also shall blow the trumpets around the whole camp, and shall say, For Jehovah and for Gideon!
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
And Gideon, and the hundred men that were with him, came to the outside of the camp in the beginning of the middle watch; and they had but newly set the watch; and they blew the trumpets, and broke the pitchers that were in their hands.
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
And the three companies blew the trumpets, and broke in pieces the pitchers, and held the torches in their left hand, and the trumpets in their right hand for blowing, and cried, The sword of Jehovah and of Gideon!
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
And they stood every man in his place round about the camp; and all the host ran, and cried out, and fled.
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
And the three hundred blew the trumpets, and Jehovah set every man's sword against his fellow, even throughout the camp. And the host fled to Beth-shittah towards Zererah, to the border of Abel-meholah, by Tabbath.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
And the men of Israel were called together out of Naphtali, and out of Asher, and out of all Manasseh, and pursued after Midian.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
And Gideon sent messengers throughout mount Ephraim, saying, Come down against Midian, and take before them the waters unto Beth-barah, and the Jordan. And all the men of Ephraim were called together, and took the waters unto Beth-barah, and the Jordan.
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
And they took two princes of Midian, Oreb and Zeeb; and they slew Oreb upon the rock Oreb, and Zeeb they slew at the winepress of Zeeb; and they pursued Midian, and brought the heads of Oreb and Zeeb to Gideon beyond the Jordan.