< Mahukunta 6 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, sai ya ba da su ga Midiyawa shekara bakwai.
Os filhos de Israel fizeram o que era mau aos olhos de Iavé, então Iavé os entregou na mão de Midian sete anos.
2 Da Midiyawa suka matsa musu sosai, sai Isra’ilawa suka yi wa kansu mafakai a rammukan duwatsu, kogona da kuma mafaka.
A mão de Midian prevaleceu contra Israel; e por causa de Midian os filhos de Israel fizeram para si os covis que estão nas montanhas, as cavernas e as fortalezas.
3 Duk lokacin da Isra’ilawa suka yi shuka sai Midiyawa da Amalekawa da waɗansu mutane daga gabashi sukan kai musu hari.
Assim foi, quando Israel semeou, que os midianitas, os amalequitas e as crianças do oriente se depararam com eles.
4 Sukan yi sansani a ƙasar sun lalatar da hatsi har zuwa Gaza kuma ba sa barin wani abu mai rai wa Isra’ila, ko tumaki ko shanu ko jakuna.
Eles acamparam contra eles, e destruíram o aumento da terra, até chegarem a Gaza. Eles não deixaram sustento em Israel, nem ovelhas, bois ou burros.
5 Sukan zo da dabbobinsu da tentinsu kamar tarin fāri. Yana da wuya a ƙidaya yawan mutanen da kuma raƙumansu; sukan mamaye ƙasar don su lalatar da ita.
Pois eles surgiram com seu gado e suas tendas. Eles vieram como gafanhotos para a multidão. Tanto eles como seus camelos eram sem número; e entraram na terra para destruí-la.
6 Midiyawa suka talauce Isra’ilawa ƙwarai, har ya sa suka yi kuka ga Ubangiji don taimako.
Israel foi trazido muito baixo por causa do Midian; e os filhos de Israel gritaram a Javé.
7 Sa’ad da Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda Midiyawa,
Quando os filhos de Israel gritaram a Javé por causa de Midian,
8 sai ya aika musu da annabi, wanda ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce na fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
Javé enviou um profeta aos filhos de Israel; e ele lhes disse: “Javé, o Deus de Israel, diz: 'Eu vos criei do Egito e vos tirei da casa da servidão.
9 Na ƙwace ku daga ikon Masarawa da kuma daga dukan hannuwan masu danniya. Na kore su a gabanku na kuma ba ku ƙasarsu.
Eu vos libertei da mão dos egípcios e da mão de todos os que vos oprimiram, e os expulsei de diante de vós, e vos dei sua terra”.
10 Na ce muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku; kada ku bauta allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a ƙasarsu.’ Amma ba ku saurare ni ba.”
Eu vos disse: “Eu sou Yahweh, vosso Deus”. Não temereis os deuses dos amorreus, em cuja terra habitais”. Mas vós não ouvistes minha voz”.”
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen oak a Ofra na Yowash mutumin Abiyezer, inda ɗansa Gideyon yake sussukar alkama a wurin matsin inabi don yă ɓoye daga Midiyawa.
O anjo de Yahweh veio e sentou-se sob o carvalho que estava em Ophrah, que pertencia a Joash, o Abiezrita. Seu filho Gideon estava batendo o trigo no lagar, para escondê-lo dos midianitas.
12 Sa’ad da mala’ikan Ubangiji ya bayyana wa Gideyon, sai ya ce masa, “Ubangiji yana tare da kai, jarumi.”
O anjo de Yahweh apareceu-lhe, e disse-lhe: “Yahweh está contigo, homem poderoso e valoroso”!
13 Gideyon ya ce, “Ranka yă daɗe, in Ubangiji yana tare da mu, me ya sa waɗannan abubuwa suka faru da mu? Ina dukan abubuwan al’ajabinsa waɗanda kakanninmu suka gaya mana game su sa’ad da suka ce, ‘Ashe, ba Ubangiji ne ya fitar da mu daga Masar ba?’ Amma yanzu Ubangiji ya rabu da mu ya kuma sa mu hannun Midiyawa.”
Gideon disse-lhe: “Oh, meu senhor, se Yahweh está conosco, por que então tudo isso aconteceu conosco? Onde estão todas as suas obras maravilhosas de que nossos pais nos falaram, dizendo: “Javé não nos trouxe do Egito? Mas agora Javé nos expulsou e nos entregou nas mãos de Midian”.
14 Sai Ubangiji ya juya wajensa ya ce, “Ka je da ƙarfin da kake da shi ka ceci Isra’ila daga hannun Midiyawa. Ba Ni ne nake aikan ka ba?”
Yahweh olhou para ele, e disse: “Vá nesta força, e salve Israel da mão de Midian. Eu não o enviei?”
15 Gideyon ya ce, “Amma Ubangiji, yaya zan iya ceci Isra’ila? Kabilata ce marar ƙarfi duka a Manasse, kuma ni ne ƙarami a iyalina.”
Ele lhe disse: “Ó Senhor, como salvar Israel? Eis que minha família é a mais pobre de Manasseh, e eu sou o menor na casa de meu pai”.
16 Ubangiji ya ce, “Zan kasance tare da kai, za ka kuwa fatattake dukan Midiyawa gaba ɗaya.”
Yahweh disse-lhe: “Certamente eu estarei com você, e você golpeará os midianitas como um só homem”.
17 Gideyon ya ce, “In lalle na sami tagomashi a gabanka, to, ka ba ni wata alamar da ta nuna lalle kai kake magana da ni.
Ele lhe disse: “Se agora encontrei um favor em sua visão, então me mostre um sinal de que é você quem fala comigo”.
18 Ina roƙonka ka dakata har in komo in kawo maka hadayata in ajiye a gabanka.” Sai Ubangiji ya ce, “Zan jira har ka dawo.”
Por favor, não vá embora até que eu venha até você, traga meu presente e o coloque diante de você”. Ele disse: “Vou esperar até você voltar”.
19 Sai Gideyon ya shiga ciki, ya gyara’yar akuya ya dafa, da garin efa ya yi burodi marar yisti. Da ya sa naman a kwando, romon kuma a tukunya, sai ya fito da su waje ya miƙa masa su a ƙarƙashin itacen oak.
Gideon entrou e preparou um cabrito jovem e bolos ázimos de uma efa de refeição. Ele colocou a carne em uma cesta e colocou o caldo em uma panela, levou-o para fora debaixo do carvalho e o apresentou.
20 Mala’ikan Allah ya ce masa, “Ka ɗauko naman da burodi marar yisti ka sa su a kan wannan dutse, ka zuba romon a kai.” Gideyon kuwa ya yi haka.
O anjo de Deus lhe disse: “Pegue a carne e os bolos ázimos, ponha-os sobre esta pedra e derrame o caldo”. Ele o fez.
21 Da kan sandan da yake a hannunsa, mala’ikan Ubangiji ya taɓa naman da burodi marar yistin. Sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da burodin. Mala’ikan kuwa ya ɓace.
Então o anjo de Yahweh estendeu a ponta do bastão que estava em sua mão e tocou a carne e os bolos ázimos; e o fogo saiu da rocha e consumiu a carne e os bolos ázimos. Então o anjo de Yahweh saiu de sua vista.
22 Sa’ad da Gideyon ya gane mala’ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka! Na ga mala’ikan Ubangiji ido da ido.”
Gideon viu que ele era o anjo de Yahweh; e Gideon disse: “Ai de mim, Senhor Yahweh! Porque eu vi o anjo de Javé cara a cara”!
23 Amma Ubangiji ya ce masa, “Salama! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.”
Yahweh disse a ele: “Que a paz esteja com você! Não tenha medo. Não morrereis”.
24 Saboda haka Gideyon ya gina wa Ubangiji bagade a can, ya kuma kira shi, Ubangiji Salama ne. Har wa yau bagaden yana a Ofra ta mutanen Abiyezer.
Então Gideon construiu ali um altar para Yahweh, e o chamou de “Yahweh é Paz”. Até hoje ainda se encontra em Ophrah dos Abiezrites.
25 A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimi na biyu daga garken mahaifinka, wannan mai shekara bakwai. Ka rushe bagaden mahaifinka na Ba’al ka sare ginshiƙin Ashera kusa da ita.
Naquela mesma noite, Yahweh disse-lhe: “Pegue o touro de seu pai, mesmo o segundo touro de sete anos, e jogue o altar de Baal que seu pai tem, e corte o Asherah que está por ele”.
26 Sa’an nan ka gina bagade irin da ya dace wa Ubangiji Allahnka a kan wannan tudu. Ka yi amfani da itacen katakon ginshiƙin Ashera da ka sare, ka miƙa bijiman nan biyu hadaya ta ƙonawa.”
Então construa um altar a Javé seu Deus no topo deste reduto, de maneira ordeira, e tome o segundo touro, e ofereça um holocausto com a madeira do Asherah que você cortará”.
27 Saboda haka Gideyon ya ɗebi bayinsa bakwai ya yi yadda Ubangiji ya ce masa. Amma saboda yana tsoron iyalinsa da mutanen gari, ya yi haka da dare a maimako da rana.
Então Gideon pegou dez homens de seus criados e fez como Yahweh havia falado com ele. Como ele temia a casa de seu pai e os homens da cidade, ele não podia fazê-lo de dia, mas o fazia de noite.
28 Da safe sa’ad da mutanen garin suka tashi, sai suka tarar an rushe bagaden Ba’al, tare da ginshiƙin Ashera da yake kusa da shi, duk an sare, bijimi na biyu kuma aka miƙa hadaya a kan sabon bagaden!
Quando os homens da cidade se levantaram cedo pela manhã, eis que o altar de Baal foi derrubado, e o Asherah foi cortado por ele, e o segundo touro foi oferecido sobre o altar que foi construído.
29 Sai suka tambayi junansu, “Wa ya yi wannan?” Sa’ad da suka bincika a hankali, sai aka faɗa musu, “Gideyon ɗan Yowash ne ya yi haka.”
Disseram um ao outro: “Quem fez esta coisa?”. Quando perguntaram e perguntaram, disseram: “Gideon, o filho de Joás, fez esta coisa”.
30 Mutanen garin suka ce wa Yowash, “Ka kawo mana ɗanka. Dole yă mutu, domin ya rushe bagaden Ba’al, ya sare ginshiƙin Asheran da yake tsaye kusa da shi.”
Então os homens da cidade disseram a Joás: “Traga seu filho para fora, para que ele possa morrer, porque ele quebrou o altar de Baal, e porque ele cortou o Asherah que estava por ele”.
31 Amma Yowash ya ce wa taron da suka tayar masa, “Za ku yi hamayya domin Ba’al ne? Kuna ƙoƙari ku cece shi ne? Duk wanda ya yi faɗa saboda shi za a kashe shi kafin safe. In lalle Ba’al allah ne, zai kāre kansa sa’ad da wani ya rushe bagadensa.”
Joás disse a todos os que estavam contra ele: “Você vai lutar por Baal? Ou você vai salvá-lo? Aquele que lutará por ele, que seja morto pela manhã! Se ele é um deus, que lute por ele mesmo, porque alguém derrubou seu altar”!
32 Saboda haka a ranar suka kira Gideyon, “Yerub-Ba’al,” suna cewa, “Bari Ba’al ya yi hamayya da shi,” domin ya rushe bagaden Ba’al.
Portanto, naquele dia ele o nomeou Jerub-Baal, dizendo: “Que Baal lute contra ele, porque ele quebrou seu altar”.
33 To, dukan Midiyawa, Amalekawa da sauran mutanen gabashi suka haɗa ƙarfi suka ƙetare Urdun suka kafa sansani a Kwarin Yezireyel.
Então todos os midianitas e os amalequitas e as crianças do leste se reuniram; e passaram, e acamparam no vale de Jezreel.
34 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Gideyon, ya kuma busa ƙaho, ya kira mutanen Abiyezer su bi shi.
Mas o Espírito de Yahweh veio sobre Gideon, e ele soou uma trombeta; e Abiezer foi reunido para segui-lo.
35 Ya aika manzanni ko’ina a Manasse, yana kiransu su kintsa, haka ma Asher, Zebulun da Naftali, ta haka su ma suka haura su sadu da su.
Ele enviou mensageiros por toda Manasseh, e eles também se reuniram para segui-lo. Ele enviou mensageiros para Asher, para Zebulun, e para Naftali; e eles vieram ao seu encontro.
36 Gideyon ya cewa Allah, “In za ka ceci Isra’ila ta hannuna yadda ka yi alkawari,
Gideon disse a Deus: “Se você salvar Israel pela minha mão, como você falou,
37 to, zan shimfiɗa ulu a masussuka, inda safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, to, zan san cewa za ka ceci Isra’ila ta hannuna, yadda ka ce.”
eis que colocarei um velo de lã na eira. Se houver orvalho somente no velo, e ele estiver seco em todo o chão, então saberei que você salvará Israel pela minha mão, como você falou”.
38 Abin da faru ke nan. Gideyon ya tashi da sassafe kashegari, ya matse ulun ya kakkaɓe raɓar, ruwan ya cika ƙwarya.
Foi assim; pois ele se levantou cedo no dia seguinte, pressionou o velo e espremeu o orvalho do velo, uma bacia cheia de água.
39 Sa’an nan Gideyon ya ce wa Allah, “Kada ka yi fushi da ni. Bari in ƙara yin wani gwaji kuma da ulun. A wannan lokaci ka sa ulun yă bushe, ƙasar kuma ta rufu da raɓa.”
Gideon disse a Deus: “Não deixe que sua raiva se acenda contra mim, e eu falarei apenas desta vez”. Por favor, deixe-me fazer um julgamento só desta vez com o velo”. Que agora esteja seco somente no velo, e em todo o chão que haja orvalho”.
40 A wannan dare Allah ya yi haka. Ulun ne kaɗai yake a bushe, amma dukan ƙasar ta jiƙe da raɓa.
Deus o fez naquela noite; pois estava seco apenas no velo, e havia orvalho em todo o chão.

< Mahukunta 6 >