< Mahukunta 6 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, sai ya ba da su ga Midiyawa shekara bakwai.
Les fils d'Israël firent encore le mal devant le Seigneur, et le Seigneur les livra aux mains de Madian, pendant sept années.
2 Da Midiyawa suka matsa musu sosai, sai Isra’ilawa suka yi wa kansu mafakai a rammukan duwatsu, kogona da kuma mafaka.
Et la main de Madian prévalut sur Israël; et les fils d'Israël, à l'aspect de Madian, se firent des cachettes dans les montagnes; ils se firent des grottes et des murs de défense dans les rochers.
3 Duk lokacin da Isra’ilawa suka yi shuka sai Midiyawa da Amalekawa da waɗansu mutane daga gabashi sukan kai musu hari.
Quand les fils d'Israël avaient semé, Madian montait avec Amalec; les fils de l'Orient marchaient dans leurs rangs, et ils campaient chez eux,
4 Sukan yi sansani a ƙasar sun lalatar da hatsi har zuwa Gaza kuma ba sa barin wani abu mai rai wa Isra’ila, ko tumaki ko shanu ko jakuna.
Et ils détruisaient leurs fruits jusqu'aux portes de Gaza, et ils ne laissèrent rien de ce qui sert à la vie en la terre d'Israël, et ils n'épargnaient ni bœuf ni âne parmi les troupeaux,
5 Sukan zo da dabbobinsu da tentinsu kamar tarin fāri. Yana da wuya a ƙidaya yawan mutanen da kuma raƙumansu; sukan mamaye ƙasar don su lalatar da ita.
Parce qu'ils montaient avec tous leurs biens et avec leurs tentes, nombreux comme des sauterelles lorsqu'elles foisonnent; leur multitude et celle de leurs chameaux étaient innombrables; ils dominaient sur la terre d'Israël, et ils la dévastaient.
6 Midiyawa suka talauce Isra’ilawa ƙwarai, har ya sa suka yi kuka ga Ubangiji don taimako.
Israël était tout appauvri devant la face de Madian. Et les fils d'Israël crièrent au Seigneur,
7 Sa’ad da Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda Midiyawa,
Et il advint ensuite que
8 sai ya aika musu da annabi, wanda ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce na fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
Et le Seigneur envoya un prophète aux fils d'Israël, et l'homme leur dit: Voici ce que dit le Seigneur Dieu d'Israël: Je suis Celui qui vous ai tirés de la terre d'Egypte, qui vous ai fait sortir de votre maison de servitude.
9 Na ƙwace ku daga ikon Masarawa da kuma daga dukan hannuwan masu danniya. Na kore su a gabanku na kuma ba ku ƙasarsu.
Je vous ai arrachés des mains de l'Egyptien et de tous ceux qui vous opprimaient; j'ai banni ceux-ci de devant votre face, et je vous ai donné leur territoire.
10 Na ce muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku; kada ku bauta allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a ƙasarsu.’ Amma ba ku saurare ni ba.”
Et je vous ai dit: Je suis le Seigneur votre Dieu; n'ayez point crainte des dieux des Amorrhéens, parmi lesquels vous résiderez en leur terre. Mais vous n'avez pas été dociles à ma voix.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen oak a Ofra na Yowash mutumin Abiyezer, inda ɗansa Gideyon yake sussukar alkama a wurin matsin inabi don yă ɓoye daga Midiyawa.
Ensuite, un ange du Seigneur vint, et il s'arrêta sous le térébinthe d'Ephratha, en la terre de Joas, fils d'Esdri, comme son fils Gédéon battait du blé dans le pressoir pour échapper aux regards des Madianites.
12 Sa’ad da mala’ikan Ubangiji ya bayyana wa Gideyon, sai ya ce masa, “Ubangiji yana tare da kai, jarumi.”
L'ange du Seigneur lui apparut, et il lui dit: Le Seigneur est avec toi, fort parmi les plus vaillants.
13 Gideyon ya ce, “Ranka yă daɗe, in Ubangiji yana tare da mu, me ya sa waɗannan abubuwa suka faru da mu? Ina dukan abubuwan al’ajabinsa waɗanda kakanninmu suka gaya mana game su sa’ad da suka ce, ‘Ashe, ba Ubangiji ne ya fitar da mu daga Masar ba?’ Amma yanzu Ubangiji ya rabu da mu ya kuma sa mu hannun Midiyawa.”
Et Gédéon dit: Je vous prie, mon Seigneur; si le Seigneur est avec nous, pourquoi ces maux nous sont-ils venus? Et où sont tous ces miracles que nous ont racontés nos pères, disant: N'est-ce point le Seigneur qui nous a fait sortir de l'Egypte? Maintenant, il nous a renversés, il nous a livrés aux mains de Madian.
14 Sai Ubangiji ya juya wajensa ya ce, “Ka je da ƙarfin da kake da shi ka ceci Isra’ila daga hannun Midiyawa. Ba Ni ne nake aikan ka ba?”
L'ange du Seigneur le regarda, et lui dit: Marche en ta force, et tu délivreras Israël des mains de Madian. Voilà que pour cela je t'envoie.
15 Gideyon ya ce, “Amma Ubangiji, yaya zan iya ceci Isra’ila? Kabilata ce marar ƙarfi duka a Manasse, kuma ni ne ƙarami a iyalina.”
Et Gédéon lui dit: Je vous prie, mon Seigneur, et comment sauverai-je Israël? Voilà que mes mille hommes sont sans force dans Manassé, et je suis le moindre de la maison de mon père.
16 Ubangiji ya ce, “Zan kasance tare da kai, za ka kuwa fatattake dukan Midiyawa gaba ɗaya.”
L'ange reprit: Le Seigneur sera avec toi, et tu vaincras Madian comme un seul homme.
17 Gideyon ya ce, “In lalle na sami tagomashi a gabanka, to, ka ba ni wata alamar da ta nuna lalle kai kake magana da ni.
Et Gédéon lui dit: Si j'ai trouvé miséricorde à vos yeux, et si vous accomplissez aujourd'hui par moi tout ce que vous m'avez promis,
18 Ina roƙonka ka dakata har in komo in kawo maka hadayata in ajiye a gabanka.” Sai Ubangiji ya ce, “Zan jira har ka dawo.”
Ne vous éloignez pas d'ici que je n'y revienne; j'apporterai une victime, et je la sacrifierai devant vous. Et l'ange répondit: Je vais rester jusqu'à ton retour.
19 Sai Gideyon ya shiga ciki, ya gyara’yar akuya ya dafa, da garin efa ya yi burodi marar yisti. Da ya sa naman a kwando, romon kuma a tukunya, sai ya fito da su waje ya miƙa masa su a ƙarƙashin itacen oak.
Gédéon rentra donc; il prépara un chevreau, et des pains sans levain d'une mesure de farine (éphi); il mit les chairs sur une corbeille, il versa le jus dans un vase; il porta tout cela à l'ange sous le térébinthe, et il s'approcha de lui.
20 Mala’ikan Allah ya ce masa, “Ka ɗauko naman da burodi marar yisti ka sa su a kan wannan dutse, ka zuba romon a kai.” Gideyon kuwa ya yi haka.
Et l'ange de Dieu lui dit: Prends les chairs et les azymes, dépose-les sur cette pierre, et répands le jus par-dessus; ainsi fit Gédéon.
21 Da kan sandan da yake a hannunsa, mala’ikan Ubangiji ya taɓa naman da burodi marar yistin. Sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da burodin. Mala’ikan kuwa ya ɓace.
Et l'ange du Seigneur étendit le bout de la baguette qu'il tenait à la main; il toucha les chairs et les azymes, et il s'éleva de la pierre une flamme qui dévora les chairs et les azymes; et l'ange du Seigneur disparut à ses yeux.
22 Sa’ad da Gideyon ya gane mala’ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka! Na ga mala’ikan Ubangiji ido da ido.”
Gédéon vit ainsi que c'était un ange du Seigneur, et il dit: Hélas! hélas! Seigneur, mon Seigneur, j'ai vu face à face un ange du Seigneur.
23 Amma Ubangiji ya ce masa, “Salama! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.”
Et le Seigneur lui dit: La paix soit avec toi; n'aie point crainte, tu ne mourras point.
24 Saboda haka Gideyon ya gina wa Ubangiji bagade a can, ya kuma kira shi, Ubangiji Salama ne. Har wa yau bagaden yana a Ofra ta mutanen Abiyezer.
Gédéon éleva en ce lieu un autel au Seigneur, et il le nomma la Paix du Seigneur, comme on le nomme de nos jours, car il subsiste encore en Ephratha, ville du père Esdri.
25 A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimi na biyu daga garken mahaifinka, wannan mai shekara bakwai. Ka rushe bagaden mahaifinka na Ba’al ka sare ginshiƙin Ashera kusa da ita.
Cette nuit même il advint que le Seigneur dit à Gédéon: Prends le taureau de ton père, avec une seconde tête de sept ans; puis tu renverseras l'autel de Baal appartenant à ton père, et tu détruiras le bois sacré qui est tout auprès;
26 Sa’an nan ka gina bagade irin da ya dace wa Ubangiji Allahnka a kan wannan tudu. Ka yi amfani da itacen katakon ginshiƙin Ashera da ka sare, ka miƙa bijiman nan biyu hadaya ta ƙonawa.”
Cela fait, tu élèveras un autel au Seigneur ton Dieu sur la cime de ce mont Maozi, en signe de résistance; tu prendras la seconde tête de bétail, et tu l'offriras comme holocauste, en la brûlant avec les arbres du bois sacré que tu auras détruit.
27 Saboda haka Gideyon ya ɗebi bayinsa bakwai ya yi yadda Ubangiji ya ce masa. Amma saboda yana tsoron iyalinsa da mutanen gari, ya yi haka da dare a maimako da rana.
Gédéon prit dix de ses serviteurs, et il fit ce que le Seigneur lui avait dit. Or, comme il craignait, à cause de la maison de son père et des hommes de la ville, de le faire en plein jour, il le fit la nuit.
28 Da safe sa’ad da mutanen garin suka tashi, sai suka tarar an rushe bagaden Ba’al, tare da ginshiƙin Ashera da yake kusa da shi, duk an sare, bijimi na biyu kuma aka miƙa hadaya a kan sabon bagaden!
Les hommes de la ville se levèrent de grand matin, et voilà que l'autel de Baal était renversé, et le bois sacré situé tout auprès détruit; et ils virent la seconde tête de bétail que Gédéon avait offerte, sur l'autel qu'il avait élevé.
29 Sai suka tambayi junansu, “Wa ya yi wannan?” Sa’ad da suka bincika a hankali, sai aka faɗa musu, “Gideyon ɗan Yowash ne ya yi haka.”
Chacun dit à son voisin: Qui a fait cela? ils s'informèrent, et ils apprirent que c'était Gédéon, fils de Joas.
30 Mutanen garin suka ce wa Yowash, “Ka kawo mana ɗanka. Dole yă mutu, domin ya rushe bagaden Ba’al, ya sare ginshiƙin Asheran da yake tsaye kusa da shi.”
Les hommes de la ville dirent alors à Joas: Amène-nous ton fils; qu'il soit mis à mort, parce qu'il a renversé l'autel de Baal et qu'il a détruit le bois sacré situé auprès.
31 Amma Yowash ya ce wa taron da suka tayar masa, “Za ku yi hamayya domin Ba’al ne? Kuna ƙoƙari ku cece shi ne? Duk wanda ya yi faɗa saboda shi za a kashe shi kafin safe. In lalle Ba’al allah ne, zai kāre kansa sa’ad da wani ya rushe bagadensa.”
Et Gédéon, fils de Joas, dit à tous les hommes de la ville, qui s'étaient soulevés contre lui: Allez-vous plaider pour Baal? est-ce vous qui le sauverez? Que celui qui plaidera pour Baal soit mis à mort avant le lever du jour. Si Baal est Dieu, qu'il se venge, puisqu'on a renversé son autel.
32 Saboda haka a ranar suka kira Gideyon, “Yerub-Ba’al,” suna cewa, “Bari Ba’al ya yi hamayya da shi,” domin ya rushe bagaden Ba’al.
Et il se donna à lui-même ce jour-là le nom de Jérobaal, en disant: Que Baal se venge, puisque son autel a été renversé.
33 To, dukan Midiyawa, Amalekawa da sauran mutanen gabashi suka haɗa ƙarfi suka ƙetare Urdun suka kafa sansani a Kwarin Yezireyel.
En ce temps-là, Madian, Amalec, et les fils de l'Orient, étaient rassembles tous à la fois; ils campaient dans la vallée de Jezraël;
34 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Gideyon, ya kuma busa ƙaho, ya kira mutanen Abiyezer su bi shi.
Et l'esprit du Seigneur vint en Gédéon; il fit sonner du cor, et sur ses pas Abiézer accourut à son secours.
35 Ya aika manzanni ko’ina a Manasse, yana kiransu su kintsa, haka ma Asher, Zebulun da Naftali, ta haka su ma suka haura su sadu da su.
Alors, il dépêcha des messagers à tout Manassé, a Azer, à Zabulon et à Nephthali, et il marcha au-devant des hommes de ces tribus.
36 Gideyon ya cewa Allah, “In za ka ceci Isra’ila ta hannuna yadda ka yi alkawari,
Et Gédéon dit à Dieu: Si votre volonté est de sauver par ma main Israël, comme vous avez dit,
37 to, zan shimfiɗa ulu a masussuka, inda safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, to, zan san cewa za ka ceci Isra’ila ta hannuna, yadda ka ce.”
Voyez: je dépose dans l'aire cette toison de laine; que la rosée se montre sur la toison seule et qu'il y ait sécheresse sur toute la terre, et je reconnaîtrai votre volonté de sauver par ma main Israël, comme vous avez dit.
38 Abin da faru ke nan. Gideyon ya tashi da sassafe kashegari, ya matse ulun ya kakkaɓe raɓar, ruwan ya cika ƙwarya.
Il en fut ainsi. Gédéon se leva de grand matin; il pressa la toison, la rosée coula de la laine, et remplit d'eau un bassin.
39 Sa’an nan Gideyon ya ce wa Allah, “Kada ka yi fushi da ni. Bari in ƙara yin wani gwaji kuma da ulun. A wannan lokaci ka sa ulun yă bushe, ƙasar kuma ta rufu da raɓa.”
Ensuite, Gédéon dit à Dieu: Que votre courroux ne s'enflamme point contre moi, et je parlerai une seule fois encore, je ferai une seule fois encore l'épreuve de la toison: que la sécheresse se montre sur la toison seule, et la rosée sur toute la terre.
40 A wannan dare Allah ya yi haka. Ulun ne kaɗai yake a bushe, amma dukan ƙasar ta jiƙe da raɓa.
Dieu fit ainsi en cette nuit même: la sécheresse se montra sur la toison seule, et il y eut de la rosée sur toute la terre.

< Mahukunta 6 >