< Mahukunta 6 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, sai ya ba da su ga Midiyawa shekara bakwai.
Les enfants d’Israël ayant de nouveau mécontenté l’Eternel, il les abandonna pendant sept ans au pouvoir des Madianites.
2 Da Midiyawa suka matsa musu sosai, sai Isra’ilawa suka yi wa kansu mafakai a rammukan duwatsu, kogona da kuma mafaka.
Accablés par la supériorité de Madian, les Israélites, pour y échapper, utilisèrent les creux des montagnes, les souterrains et les châteaux forts.
3 Duk lokacin da Isra’ilawa suka yi shuka sai Midiyawa da Amalekawa da waɗansu mutane daga gabashi sukan kai musu hari.
Or, quand Israël avait fait les semailles, Madian accourait avec Amalec et les peuplades orientales, et venait l’attaquer.
4 Sukan yi sansani a ƙasar sun lalatar da hatsi har zuwa Gaza kuma ba sa barin wani abu mai rai wa Isra’ila, ko tumaki ko shanu ko jakuna.
Ils occupaient son pays, détruisaient les produits de la terre jusque vers Gaza, et ne laissaient en Israël aucune subsistance, non plus que brebis, bœufs ni ânes.
5 Sukan zo da dabbobinsu da tentinsu kamar tarin fāri. Yana da wuya a ƙidaya yawan mutanen da kuma raƙumansu; sukan mamaye ƙasar don su lalatar da ita.
Car eux-mêmes venaient avec leurs troupeaux et leurs tentes, ils arrivaient en masse comme les sauterelles, eux et leurs chameaux étaient innombrables; et ils envahissaient le pays pour le ravager.
6 Midiyawa suka talauce Isra’ilawa ƙwarai, har ya sa suka yi kuka ga Ubangiji don taimako.
lsraël tomba ainsi dans une misère extrême par le fait de Madian, et il se plaignit à l’Eternel.
7 Sa’ad da Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda Midiyawa,
Comme les enfants d’Israël se plaignaient à l’Eternel au sujet de Madian,
8 sai ya aika musu da annabi, wanda ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce na fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
l’Eternel leur envoya un personnage inspiré, qui leur dit: "Ainsi a parlé l’Eternel, Dieu d’Israël: C’Est moi qui vous ai fait monter de l’Egypte, qui vous ai tirés de la maison de servitude;
9 Na ƙwace ku daga ikon Masarawa da kuma daga dukan hannuwan masu danniya. Na kore su a gabanku na kuma ba ku ƙasarsu.
je vous ai sauvés de la main des Egyptiens et de la main de vos autres oppresseurs; j’ai chassé ces derniers devant vous et vous ai donné leur pays.
10 Na ce muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku; kada ku bauta allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a ƙasarsu.’ Amma ba ku saurare ni ba.”
Et je vous ai dit: "C’Est moi, I’Eternel, qui suis votre Dieu! ne révérez point les dieux des Amorréens dont vous habitez le pays!" Mais vous n’avez pas écouté ma voix…"
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen oak a Ofra na Yowash mutumin Abiyezer, inda ɗansa Gideyon yake sussukar alkama a wurin matsin inabi don yă ɓoye daga Midiyawa.
Or, un ange du Seigneur vint se placer sous un térébinthe près d’Ofra, appartenant à Joas l’Abiézrite, au moment où Gédéon, son fils, battait du froment dans le pressoir pour le mettre à l’abri des Madianites.
12 Sa’ad da mala’ikan Ubangiji ya bayyana wa Gideyon, sai ya ce masa, “Ubangiji yana tare da kai, jarumi.”
L’Ange du Seigneur lui apparut et lui dit: "L’Eternel est avec toi, vaillant homme!"
13 Gideyon ya ce, “Ranka yă daɗe, in Ubangiji yana tare da mu, me ya sa waɗannan abubuwa suka faru da mu? Ina dukan abubuwan al’ajabinsa waɗanda kakanninmu suka gaya mana game su sa’ad da suka ce, ‘Ashe, ba Ubangiji ne ya fitar da mu daga Masar ba?’ Amma yanzu Ubangiji ya rabu da mu ya kuma sa mu hannun Midiyawa.”
Et Gédéon lui répondit: "Hélas! Seigneur, si l’Eternel est avec nous, d’où vient tout ce qui nous arrive? Que sont devenus tous ses prodiges que nous ont contés nos pères, disant: N’Est-ce pas l’Eternel qui nous a fait sortir de l’Egypte? Maintenant l’Eternel nous délaisse et nous livre aux mains de Madian!"
14 Sai Ubangiji ya juya wajensa ya ce, “Ka je da ƙarfin da kake da shi ka ceci Isra’ila daga hannun Midiyawa. Ba Ni ne nake aikan ka ba?”
Alors l’Eternel s’adressa à lui, disant: "Va avec ce courage qui t’anime, et tu sauveras Israël de la main de Madian: c’est moi qui t’envoie."
15 Gideyon ya ce, “Amma Ubangiji, yaya zan iya ceci Isra’ila? Kabilata ce marar ƙarfi duka a Manasse, kuma ni ne ƙarami a iyalina.”
Gédéon répliqua: "De grâce, mon Dieu, par quel moyen sauverais-je Israël? Ma famille est la moindre en Manassé, et moi je suis le plus jeune dans la maison de mon père!"
16 Ubangiji ya ce, “Zan kasance tare da kai, za ka kuwa fatattake dukan Midiyawa gaba ɗaya.”
"C’Est que je serai avec toi, répondit l’Eternel, et tu battras les Madianites comme un seul homme."
17 Gideyon ya ce, “In lalle na sami tagomashi a gabanka, to, ka ba ni wata alamar da ta nuna lalle kai kake magana da ni.
"Eh bien! dit-il, si j’ai trouvé faveur à tes yeux, tu me prouveras par un signe que c’est toi-même qui me parles.
18 Ina roƙonka ka dakata har in komo in kawo maka hadayata in ajiye a gabanka.” Sai Ubangiji ya ce, “Zan jira har ka dawo.”
Ne t’éloigne pas d’ici, je te prie, que je ne sois revenu près de toi: je vais quérir mon offrande et la déposer devant toi." Il répondit: "J’Attendrai ton retour."
19 Sai Gideyon ya shiga ciki, ya gyara’yar akuya ya dafa, da garin efa ya yi burodi marar yisti. Da ya sa naman a kwando, romon kuma a tukunya, sai ya fito da su waje ya miƙa masa su a ƙarƙashin itacen oak.
Et Gédéon rentra, apprêta un jeune chevreau et des pains azymes d’un êpha de farine, mit la viande dans une corbeille et le bouillon dans un pot, porta le tout sous le térébinthe et le lui offrit.
20 Mala’ikan Allah ya ce masa, “Ka ɗauko naman da burodi marar yisti ka sa su a kan wannan dutse, ka zuba romon a kai.” Gideyon kuwa ya yi haka.
L’Ange de Dieu lui dit: "Prends la viande avec les azymes, pose-les sur ce rocher, et répands le bouillon"; ce qu’il fit.
21 Da kan sandan da yake a hannunsa, mala’ikan Ubangiji ya taɓa naman da burodi marar yistin. Sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da burodin. Mala’ikan kuwa ya ɓace.
Et l’ange de l’Eternel, de l’extrémité du bâton qu’il tenait à la main, toucha la viande et les azymes: soudain un feu sortit du rocher, consuma viande et azymes, et l’ange de l’Eternel disparut à ses yeux.
22 Sa’ad da Gideyon ya gane mala’ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka! Na ga mala’ikan Ubangiji ido da ido.”
Gédéon vit alors que c’était un ange, et il s’écria: "Malheur à moi, Seigneur Dieu! car c’est un ange de l’Eternel que j’ai vu face à face."
23 Amma Ubangiji ya ce masa, “Salama! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.”
"Rassure-toi, lui dit le Seigneur, ne crains rien: tu ne mourras pas."
24 Saboda haka Gideyon ya gina wa Ubangiji bagade a can, ya kuma kira shi, Ubangiji Salama ne. Har wa yau bagaden yana a Ofra ta mutanen Abiyezer.
Gédéon bâtit là au Seigneur un autel, qu’il appela Adonaï Chalôm; aujourd’hui encore il subsiste dans Ofra, qui est aux Abiézrites.
25 A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimi na biyu daga garken mahaifinka, wannan mai shekara bakwai. Ka rushe bagaden mahaifinka na Ba’al ka sare ginshiƙin Ashera kusa da ita.
Cette même nuit, l’Eternel lui dit: "Prends l’un des taureaux qui sont à ton père, le deuxième taureau, âgé de sept ans. Tu démoliras l’autel consacré à Baal par ton père, et tu abattras le bocage qui est auprès.
26 Sa’an nan ka gina bagade irin da ya dace wa Ubangiji Allahnka a kan wannan tudu. Ka yi amfani da itacen katakon ginshiƙin Ashera da ka sare, ka miƙa bijiman nan biyu hadaya ta ƙonawa.”
Puis tu bâtiras un autel à l’Eternel, ton Dieu, au sommet de ce rocher, sur le plateau; tu prendras le deuxième taureau, et le brûleras en holocauste, sur le bois du bocage que tu auras abattu."
27 Saboda haka Gideyon ya ɗebi bayinsa bakwai ya yi yadda Ubangiji ya ce masa. Amma saboda yana tsoron iyalinsa da mutanen gari, ya yi haka da dare a maimako da rana.
Gédéon, aidé de dix de ses serviteurs, fit ce que l’Eternel lui avait ordonné; mais comme il n’osait, à cause de sa famille et des gens de la ville, agir en plein jour, il le fit nuitamment.
28 Da safe sa’ad da mutanen garin suka tashi, sai suka tarar an rushe bagaden Ba’al, tare da ginshiƙin Ashera da yake kusa da shi, duk an sare, bijimi na biyu kuma aka miƙa hadaya a kan sabon bagaden!
Au matin, quand les gens de la ville se levèrent, ils virent l’autel de Baal renversé, son bocage abattu, le deuxième taureau offert en holocauste sur l’autel nouveau,
29 Sai suka tambayi junansu, “Wa ya yi wannan?” Sa’ad da suka bincika a hankali, sai aka faɗa musu, “Gideyon ɗan Yowash ne ya yi haka.”
et ils se dirent l’un à l’autre: "Qui a fait cela?…" Ils s’informèrent, firent des recherches et on leur dit: "C’Est Gédéon, fils de Joas, qui en est l’auteur."
30 Mutanen garin suka ce wa Yowash, “Ka kawo mana ɗanka. Dole yă mutu, domin ya rushe bagaden Ba’al, ya sare ginshiƙin Asheran da yake tsaye kusa da shi.”
Alors les gens de la ville dirent à Joas: "Livre ton fils pour qu’il meure, parce qu’il a démoli l’autel de Baal et abattu le bocage attenant."
31 Amma Yowash ya ce wa taron da suka tayar masa, “Za ku yi hamayya domin Ba’al ne? Kuna ƙoƙari ku cece shi ne? Duk wanda ya yi faɗa saboda shi za a kashe shi kafin safe. In lalle Ba’al allah ne, zai kāre kansa sa’ad da wani ya rushe bagadensa.”
Mais Joas dit à la foule qui l’assaillait: "Est-ce à vous de venger Baal, à vous de lui venir en aide? Qui prétend le faire mérite la mort, avant même qu’il soit jour! Si Baal est Dieu, qu’il venge lui-même son injure, son autel renversé!"
32 Saboda haka a ranar suka kira Gideyon, “Yerub-Ba’al,” suna cewa, “Bari Ba’al ya yi hamayya da shi,” domin ya rushe bagaden Ba’al.
Gédéon fut à cette occasion, surnommé Jérubbaal, c’est-à-dire que Baal s’en prenne à lui, pour avoir démoli son autel.
33 To, dukan Midiyawa, Amalekawa da sauran mutanen gabashi suka haɗa ƙarfi suka ƙetare Urdun suka kafa sansani a Kwarin Yezireyel.
Or, tout Madian s’était réuni avec Amalec et les peuplades orientales; ils avaient pénétré à l’intérieur et campaient dans la vallée de Jezreêl.
34 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Gideyon, ya kuma busa ƙaho, ya kira mutanen Abiyezer su bi shi.
Soudain une inspiration divine enveloppa Gédéon; il fit sonner du cor, et les Abiézrites se groupèrent derrière lui.
35 Ya aika manzanni ko’ina a Manasse, yana kiransu su kintsa, haka ma Asher, Zebulun da Naftali, ta haka su ma suka haura su sadu da su.
Il envoya aussi des messagers dans tout Manassé, qui se joignit également à lui; pareillement en Aser, Zabulon, Nephtali, qui montèrent au-devant d’eux.
36 Gideyon ya cewa Allah, “In za ka ceci Isra’ila ta hannuna yadda ka yi alkawari,
Et Gédéon dit au Seigneur: "Si tu veux, par ma main, secourir Israël comme tu l’as dit,
37 to, zan shimfiɗa ulu a masussuka, inda safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, to, zan san cewa za ka ceci Isra’ila ta hannuna, yadda ka ce.”
eh bien! je mets cette toison sur le sol de l’aire: s’il vient de la rosée sur la toison seule et que tout le sol reste sec, je saurai que tu veux secourir par ma main Israël, comme tu l’as promis."
38 Abin da faru ke nan. Gideyon ya tashi da sassafe kashegari, ya matse ulun ya kakkaɓe raɓar, ruwan ya cika ƙwarya.
Et il en fut ainsi. En se levant le lendemain, Gédéon pressa la toison et, de la rosée qu’il en exprima, il eut une pleine écuelle d’eau.
39 Sa’an nan Gideyon ya ce wa Allah, “Kada ka yi fushi da ni. Bari in ƙara yin wani gwaji kuma da ulun. A wannan lokaci ka sa ulun yă bushe, ƙasar kuma ta rufu da raɓa.”
Gédéon dit au Seigneur: "Ne te mets pas en colère contre moi si je t’adresse encore une prière. Permets-moi seulement une nouvelle épreuve par cette toison: que la toison seule reste sèche, tandis que tout le sol sera couvert de rosée!"
40 A wannan dare Allah ya yi haka. Ulun ne kaɗai yake a bushe, amma dukan ƙasar ta jiƙe da raɓa.
Dieu déféra à sa demande cette nuit même: la toison seule resta sèche, le sol d’alentour fut couvert de rosée.

< Mahukunta 6 >