< Mahukunta 6 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, sai ya ba da su ga Midiyawa shekara bakwai.
Again the Israelis did things that Yahweh said were very evil. So he allowed the people of Midian to conquer them and rule them for seven years.
2 Da Midiyawa suka matsa musu sosai, sai Isra’ilawa suka yi wa kansu mafakai a rammukan duwatsu, kogona da kuma mafaka.
The people of Midian treated the Israelis so cruelly that the Israelis fled to the mountains. There they made places to live in caves and animal dens.
3 Duk lokacin da Isra’ilawa suka yi shuka sai Midiyawa da Amalekawa da waɗansu mutane daga gabashi sukan kai musu hari.
Whenever the Israelis planted things in their fields, the people of Midian and Amalek and other groups from the east invaded Israel.
4 Sukan yi sansani a ƙasar sun lalatar da hatsi har zuwa Gaza kuma ba sa barin wani abu mai rai wa Isra’ila, ko tumaki ko shanu ko jakuna.
They set up tents in the area, and then destroyed the crops as far south as Gaza. They did not leave anything for the Israelis’ sheep or cattle or donkeys to eat.
5 Sukan zo da dabbobinsu da tentinsu kamar tarin fāri. Yana da wuya a ƙidaya yawan mutanen da kuma raƙumansu; sukan mamaye ƙasar don su lalatar da ita.
They came into Israel with their tents and their livestock like a swarm of locusts. There were [so many of them that] arrived riding on their camels that no one could count them. They stayed and ruined the Israelis’ crops.
6 Midiyawa suka talauce Isra’ilawa ƙwarai, har ya sa suka yi kuka ga Ubangiji don taimako.
The people of Midian took almost everything the Israelis owned. So finally the Israelis pleaded for Yahweh to help them.
7 Sa’ad da Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda Midiyawa,
When the Israelis pleaded with Yahweh to help them because of [what] the people from Midian [were doing to them],
8 sai ya aika musu da annabi, wanda ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce na fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
he sent to them a prophet, who said, “Yahweh, the God we Israelis worship, says this: ‘Your ancestors were slaves in Egypt.
9 Na ƙwace ku daga ikon Masarawa da kuma daga dukan hannuwan masu danniya. Na kore su a gabanku na kuma ba ku ƙasarsu.
But I rescued them from the leaders of Egypt and from all the others who oppressed them. I expelled their enemies from this land, and gave it to your ancestors.
10 Na ce muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku; kada ku bauta allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a ƙasarsu.’ Amma ba ku saurare ni ba.”
I told you all, “I am Yahweh, your God. You are now in the land where the descendants of Amor live, but you must not worship the gods whom they worship.” But you did not pay attention to me.’”
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen oak a Ofra na Yowash mutumin Abiyezer, inda ɗansa Gideyon yake sussukar alkama a wurin matsin inabi don yă ɓoye daga Midiyawa.
One day Yahweh appeared [in the form of] an angel and sat underneath a big oak tree at Ophrah [town]. That tree belonged to Joash, who was from the clan of Abiezer. Joash’s son Gideon was threshing wheat in the pit where they pressed [grapes to make] wine. He was threshing the grain there in order to hide it from the people of Midian.
12 Sa’ad da mala’ikan Ubangiji ya bayyana wa Gideyon, sai ya ce masa, “Ubangiji yana tare da kai, jarumi.”
Yahweh [went over] to Gideon and said to him, “You mighty warrior, Yahweh is helping you!”
13 Gideyon ya ce, “Ranka yă daɗe, in Ubangiji yana tare da mu, me ya sa waɗannan abubuwa suka faru da mu? Ina dukan abubuwan al’ajabinsa waɗanda kakanninmu suka gaya mana game su sa’ad da suka ce, ‘Ashe, ba Ubangiji ne ya fitar da mu daga Masar ba?’ Amma yanzu Ubangiji ya rabu da mu ya kuma sa mu hannun Midiyawa.”
Gideon replied, “Sir, if Yahweh is helping us, why have all these [bad things] happened to us? We heard about [RHQ] all the miracles that Yahweh performed for our ancestors. We heard people tell us about how he rescued them from [being slaves in] Egypt. But now Yahweh has abandoned us, and we are ruled by the people from Midian.”
14 Sai Ubangiji ya juya wajensa ya ce, “Ka je da ƙarfin da kake da shi ka ceci Isra’ila daga hannun Midiyawa. Ba Ni ne nake aikan ka ba?”
Then Yahweh turned toward him and said, “I will give you strength to enable you to rescue the Israelis from the people of Midian. I am sending you [to do that]!”
15 Gideyon ya ce, “Amma Ubangiji, yaya zan iya ceci Isra’ila? Kabilata ce marar ƙarfi duka a Manasse, kuma ni ne ƙarami a iyalina.”
Gideon replied, “But Yahweh, how can I rescue the Israelis? My clan is the least significant in the whole tribe descended from Manasseh, and I am the least significant person in my whole family!”
16 Ubangiji ya ce, “Zan kasance tare da kai, za ka kuwa fatattake dukan Midiyawa gaba ɗaya.”
Yahweh said to him, “I will help you. So you will defeat the army of Midian [as easily] as if you were fighting only one man!”
17 Gideyon ya ce, “In lalle na sami tagomashi a gabanka, to, ka ba ni wata alamar da ta nuna lalle kai kake magana da ni.
Gideon replied, “If you are truly pleased with me, do something which will prove that you who are speaking to me are really Yahweh.
18 Ina roƙonka ka dakata har in komo in kawo maka hadayata in ajiye a gabanka.” Sai Ubangiji ya ce, “Zan jira har ka dawo.”
But do not go away until I go and bring back an offering to you.” Yahweh answered, “Okay, I will stay here until you return.”
19 Sai Gideyon ya shiga ciki, ya gyara’yar akuya ya dafa, da garin efa ya yi burodi marar yisti. Da ya sa naman a kwando, romon kuma a tukunya, sai ya fito da su waje ya miƙa masa su a ƙarƙashin itacen oak.
Gideon hurried to his home. He [killed] a young goat [and] cooked [it]. Then he took (a half a bushel/18 liters) of flour and baked some bread without yeast. Then he put the cooked meat in a basket, and put the broth [from the meat] in a pot, and took it to Yahweh, who was sitting under the tree.
20 Mala’ikan Allah ya ce masa, “Ka ɗauko naman da burodi marar yisti ka sa su a kan wannan dutse, ka zuba romon a kai.” Gideyon kuwa ya yi haka.
Then Yahweh said to him, “Put the meat and the bread on this rock. Then pour the broth on top of it.” So Gideon did that.
21 Da kan sandan da yake a hannunsa, mala’ikan Ubangiji ya taɓa naman da burodi marar yistin. Sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da burodin. Mala’ikan kuwa ya ɓace.
Then Yahweh touched the meat and bread with the walking stick that was in his hand. A fire flamed up from the rock and burned up everything that Gideon had brought! And then Yahweh disappeared.
22 Sa’ad da Gideyon ya gane mala’ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka! Na ga mala’ikan Ubangiji ido da ido.”
When Gideon realized that it was really Yahweh [who had appeared in the form of an angel and talked with him], he exclaimed, “O, Yahweh, I have seen you face-to-face [when you had the form of] an angel! [So I will surely die]!”
23 Amma Ubangiji ya ce masa, “Salama! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.”
But Yahweh called to him and said, “Do not be afraid! You will not die [because of seeing me]!”
24 Saboda haka Gideyon ya gina wa Ubangiji bagade a can, ya kuma kira shi, Ubangiji Salama ne. Har wa yau bagaden yana a Ofra ta mutanen Abiyezer.
Then Gideon built an altar to [worship] Yahweh there. He named it ‘Yahweh gives us peace’. That altar is still there in Ophrah [town], in the land that belongs to the descendants of Abiezer.
25 A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimi na biyu daga garken mahaifinka, wannan mai shekara bakwai. Ka rushe bagaden mahaifinka na Ba’al ka sare ginshiƙin Ashera kusa da ita.
That night Yahweh said to Gideon, “Take the second-best/oldest bull from your father’s herd, the bull that is seven years old. [Kill it]. Then tear down the altar that your father built to [worship] the god Baal. Also cut down the pole for worshipping [the goddess] Astarte that is there beside it.
26 Sa’an nan ka gina bagade irin da ya dace wa Ubangiji Allahnka a kan wannan tudu. Ka yi amfani da itacen katakon ginshiƙin Ashera da ka sare, ka miƙa bijiman nan biyu hadaya ta ƙonawa.”
Then build a [stone] altar to worship me, your God Yahweh, here on this hill. Take the wood from the pole you cut down and make a fire [to cook the meat of the bull] as a burnt offering to me.”
27 Saboda haka Gideyon ya ɗebi bayinsa bakwai ya yi yadda Ubangiji ya ce masa. Amma saboda yana tsoron iyalinsa da mutanen gari, ya yi haka da dare a maimako da rana.
So Gideon and his servants did what Yahweh commanded. But they did it at night, because he was afraid what the other members of his family and the other men in town would do to him if they found out that he had done that.
28 Da safe sa’ad da mutanen garin suka tashi, sai suka tarar an rushe bagaden Ba’al, tare da ginshiƙin Ashera da yake kusa da shi, duk an sare, bijimi na biyu kuma aka miƙa hadaya a kan sabon bagaden!
Early the next morning, as soon as the men got up, they saw that the altar to Baal had been torn down, and the pole for worshiping Astarte was gone. They saw that there was a new altar there, and on it was what remained from the bull they had sacrificed.
29 Sai suka tambayi junansu, “Wa ya yi wannan?” Sa’ad da suka bincika a hankali, sai aka faɗa musu, “Gideyon ɗan Yowash ne ya yi haka.”
The people asked each other, “Who did this?” After they investigated, someone told them that it was Gideon, the son of Joash, [who had done it].
30 Mutanen garin suka ce wa Yowash, “Ka kawo mana ɗanka. Dole yă mutu, domin ya rushe bagaden Ba’al, ya sare ginshiƙin Asheran da yake tsaye kusa da shi.”
They went to Joash and said to him, “Bring your son out here! (He must be executed/We must kill him), because he destroyed our god Baal’s altar and cut down the pole for our goddess Astarte!”
31 Amma Yowash ya ce wa taron da suka tayar masa, “Za ku yi hamayya domin Ba’al ne? Kuna ƙoƙari ku cece shi ne? Duk wanda ya yi faɗa saboda shi za a kashe shi kafin safe. In lalle Ba’al allah ne, zai kāre kansa sa’ad da wani ya rushe bagadensa.”
But Joash replied, “Are you trying to defend Baal? Are you trying to argue his case? Anyone who tries to defend Baal should be executed by tomorrow morning! If Baal is truly a god, he ought to be able to defend himself, and to get rid of the person who tore down his altar!”
32 Saboda haka a ranar suka kira Gideyon, “Yerub-Ba’al,” suna cewa, “Bari Ba’al ya yi hamayya da shi,” domin ya rushe bagaden Ba’al.
From that time, people called Gideon Jerub-Baal, which means ‘Baal should defend himself’, because he tore down Baal’s altar.
33 To, dukan Midiyawa, Amalekawa da sauran mutanen gabashi suka haɗa ƙarfi suka ƙetare Urdun suka kafa sansani a Kwarin Yezireyel.
Soon after that, the armies of the people of Midian and of Amalek and the people from the east gathered together. They crossed the Jordan River [to attack the Israelis]. They set up their tents in Jezreel Valley.
34 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Gideyon, ya kuma busa ƙaho, ya kira mutanen Abiyezer su bi shi.
Then Yahweh’s Spirit took control of Gideon. He blew a ram’s horn to summon the men to prepare to fight. So the men of the clan of Abiezer came to him.
35 Ya aika manzanni ko’ina a Manasse, yana kiransu su kintsa, haka ma Asher, Zebulun da Naftali, ta haka su ma suka haura su sadu da su.
He also sent messengers throughout the tribes descended from [the four tribes of] Manasseh, Asher, Zebulun, and Naphtali [to tell their soldiers to come], and all of them came.
36 Gideyon ya cewa Allah, “In za ka ceci Isra’ila ta hannuna yadda ka yi alkawari,
Then Gideon said to God, “If you are truly going to enable me to rescue the Israeli people as you promised,
37 to, zan shimfiɗa ulu a masussuka, inda safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, to, zan san cewa za ka ceci Isra’ila ta hannuna, yadda ka ce.”
confirm it by doing this: Tonight I will put a dry wool fleece on the ground where I thresh the grain. Tomorrow morning, if the fleece is wet with dew but the ground is dry, then I will know that I am the one you will enable to rescue the people of Israel as you promised.”
38 Abin da faru ke nan. Gideyon ya tashi da sassafe kashegari, ya matse ulun ya kakkaɓe raɓar, ruwan ya cika ƙwarya.
And that is what happened. When Gideon got up the next morning, he picked up the fleece, and squeezed out a whole bowlful of water!
39 Sa’an nan Gideyon ya ce wa Allah, “Kada ka yi fushi da ni. Bari in ƙara yin wani gwaji kuma da ulun. A wannan lokaci ka sa ulun yă bushe, ƙasar kuma ta rufu da raɓa.”
Then Gideon said to God, “Do not be angry with me, but let me ask you to do one more thing. Tonight I will put the fleece out again. This time, let the fleece remain dry, while the ground is wet with the dew.”
40 A wannan dare Allah ya yi haka. Ulun ne kaɗai yake a bushe, amma dukan ƙasar ta jiƙe da raɓa.
So that night, God did what Gideon asked him to do. The next morning the fleece was dry, but the ground was covered with dew.

< Mahukunta 6 >