< Mahukunta 5 >
1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
Då söngo Deborah och Barak, AbiNoams son, på den samma tiden, och sade:
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
Lofver Herran, att Israel är åter fri vorden, och folket hafver varit der viljogt till.
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Hörer till, I Konungar, och akter uppå, I Förstar: jag vill, Herranom vill jag sjunga, Herranom Israels Gudi vill jag spela.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
Herre, då du utdrogst ifrå Seir, och gick fram ifrån Edoms mark, då skalf jorden, himmelen dröp, och skyarna dröpo vatten.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Bergen smulto för Herranom, Sinai för Herranom Israels Gud.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
I Samgars, Anaths sons, tid, i Jaels tid, voro vägarna förgångne; och de som på stigarna gå skulle, de vandrade krokota vägar.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
Det fattades, bönder fattades i Israel, tilldess jag Debora uppkom, tilldess jag uppkom en moder i Israel.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
Ett nytt hafver Gud utvalt, portarna hafver han bestridt; ingen sköld eller spets vardt sedd ibland fyratiotusend i Israel.
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
Mitt hjerta faller till Israels regenter, hvilke friviljoge äro ibland folket.
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
Lofver Herran, I som riden på sköna åsninnor, I som sitten för rätta; och sjunger, I som gån på vägomen.
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
Der skyttarna ropa ibland dem som vatten hemta, der säge man om Herrans rättfärdighet, om hans bönders rättfärdighet i Israel; då drog Herrans folk neder till portarna.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
Upp, upp, Debora, upp, upp, och sjung ena viso; upp, Barak, och fånga dina fångare, du AbiNoams son.
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
Då vordo de förlåtne rådande öfver de mägtiga; Herren vardt rådandes genom mig öfver de hjeltar.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
Utaf Ephraim var deras rot emot Amalek; och efter dig BenJamin i ditt folk. Af Machir äro komne regenter; och af Sebulon äro regerare vordne igenom skrifpennan.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
Isaschars Förstar voro med Debora, och Isaschar var såsom Barak i dalenom, utsänder med sitt fotfolk. Ruben höll mycket af sig, och skiljde sig ifrån oss.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Hvi blefst du i dinom fårahyddom, till att höra hjordarnas bräkande; och höll mycket af dig, och skiljde dig ifrån oss?
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Gilead blef hinsidon Jordan. Och hvi bor Dan ibland skeppen? Asser satt i hafsens hamn, och blef i sina förfallna byar.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Men Sebulons folk vågade sina själ i döden; Naphthali desslikes på höjdene af markene.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
Konungarna kommo och stridde. Då stridde de Cananeers Konungar i Thaanach, vid det vattnet Megiddo; men de hade ingen vinning deraf.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
Af himmelen var stridt emot dem; stjernorna i deras lopp stridde emot Sisera.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
Den bäcken Kison vältrade dem, den bäcken Kedumim, den bäcken Kison. Träd, min själ, på de starka.
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
Då darrade hästarnas fötter, för deras starka åsittares förfärelses skull.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
Förbanner den staden Meros, sade Herrans Ängel; förbanner hans borgare, att de icke kommo Herranom till hjelp; till hjelp Herranom, till de hjeltar.
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Välsignad vare ibland qvinnor Jael, Hebers den Kenitens hustru; välsignad vare hon i hyddomen ibland qvinnor.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
Mjölk gaf hon, då han vatten beddes, och bar smör in uti en härlig skål.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
Hon tog naglan med sin hand, och smedshammaren i sina högra hand, och slog Sisera genom hans hufvud; sönderkrossade, och genomstack hans tinningar.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
Till hennes fötter krökte han sig, föll neder, och lade sig; han krökte sig, och föll neder till hennes fötter; såsom han krökte sig, så låg han förderfvad.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
Sisera moder såg genom fenstret ut, och gret igenom gallren: Hvi förtöfvar hans vagn så länge, att han icke kommer? Hvi fördröja hans vagns hjul?
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
De visesta ibland hennes qvinnor svarade, då hon så jämmerliga qvidde:
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
Skulle de icke finna och byta rof, hvarjom manne en ung pigo eller två till byte; och Sisera brokot stickad kläder till byte, stickad brokot kläder om halsen till byte?
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
Alltså, Herre, förgånge alle dine fiender; men de som honom kär hafva, de vare såsom uppgångande solen i sine magt. Och landet hade frid i fyratio år.