< Mahukunta 5 >

1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
و در آن روز دبوره و باراق بن ابینوعم سرودخوانده، گفتند:۱
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
«چونکه پیش روان در اسرائیل پیشروی کردند، چونکه قوم نفوس خود را به ارادت تسلیم نمودند، خداوند را متبارک بخوانید.۲
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
‌ای پادشاهان بشنوید! ای زورآوران گوش دهید! من خود برای خداوند خواهم سرایید. برای یهوه خدای اسرائیل سرود خواهم خواند.۳
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
‌ای خداوند وقتی که از سعیر بیرون آمدی، وقتی که از صحرای ادوم خرامیدی، زمین متزلزل شد و آسمان نیز قطره‌ها ریخت. و ابرها هم آبهابارانید.۴
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
کوهها از حضور خداوند لرزان شد و این سینا ازحضور یهوه، خدای اسرائیل.۵
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
در ایام شمجر بن عنات، در ایام یاعیل شاهراههاترک شده بود، و مسافران از راههای غیرمتعارف می رفتند.۶
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
حاکمان در اسرائیل نایاب و نابود شدند، تا من، دبوره، برخاستم، در اسرائیل، مادر برخاستم.۷
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
خدایان جدید را اختیار کردند. پس جنگ دردروازه‌ها رسید. در میان چهل هزار نفر دراسرائیل، سپری و نیزه‌ای پیدا نشد.۸
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
قلب من به حاکمان اسرائیل مایل است، که خودرا در میان قوم به ارادت تسلیم نمودند. خداوند رامتبارک بخوانید.۹
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
‌ای شما که بر الاغهای سفید سوارید و برمسندها می‌نشینید، و بر طریق سالک هستید، این را بیان کنید.۱۰
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
دور از آواز تیراندازان، نزد حوضهای آب درآنجا اعمال عادله خداوند را بیان می‌کنند، یعنی احکام عادله او را در حکومت اسرائیل. آنگاه قوم خداوند به دروازه‌ها فرود می‌آیند.۱۱
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
بیدار شو بیدار شو‌ای دبوره. بیدار شو بیدارشو و سرود بخوان. برخیز‌ای باراق و‌ای پسرابینوعم، اسیران خود را به اسیری ببر.۱۲
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
آنگاه جماعت قلیل بر بزرگان قوم تسلطیافتند. و خداوند مرا بر جباران مسلط ساخت.۱۳
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
از افرایم آمدند، آنانی که مقر ایشان در عمالیق است. در عقب تو بنیامین با قومهای تو، و از ماکیرداوران آمدند. و از زبولون آنانی که عصای صف آرا را به‌دست می‌گیرند.۱۴
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
و سروران یساکار همراه دبوره بودند. چنانکه باراق بود همچنان یساکار نیز بود. در عقب او به وادی هجوم آوردند. فکرهای دل نزد شعوب روبین عظیم بود.۱۵
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
چرا در میان آغلها نشستی. آیا تا نی گله‌ها رابشنوی؟ مباحثات دل، نزد شعوب روبین عظیم بود.۱۶
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
جلعاد به آن طرف اردن ساکن ماند. و دان چرانزد کشتیها درنگ نمود. اشیر به کناره دریانشست. و نزد خلیجهای خود ساکن ماند.۱۷
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
و زبولون قومی بودند که جان خود را به خطرموت تسلیم نمودند. و نفتالی نیز در بلندیهای میدان.۱۸
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
پادشاهان آمده، جنگ کردند. آنگاه پادشاهان کنعان مقاتله نمودند. در تعنک نزد آبهای مجدو. و هیچ منفعت نقره نبردند.۱۹
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
از آسمان جنگ کردند. ستارگان از منازل خودبا سیسرا جنگ کردند.۲۰
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
نهر قیشون ایشان را در ربود. آن نهر قدیم یعنی نهر قیشون. ای جان من قوت را پایمال نمودی.۲۱
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
آنگاه اسبان، زمین را پازدن گرفتند. به‌سبب تاختن یعنی تاختن زورآوران ایشان.۲۲
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
فرشته خداوند می‌گوید میروز را لعنت کنید، ساکنانش را به سختی لعنت کنید، زیرا که به امدادخداوند نیامدند تا خداوند را در میان جباران اعانت نمایند.۲۳
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
یاعیل، زن حابرقینی، از سایر زنان مبارک باد! از زنان چادرنشین مبارک باد!۲۴
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
او آب خواست و شیر به وی داد، و سرشیر رادر ظرف ملوکانه پیش آورد.۲۵
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
دست خود را به میخ دراز کرد، و دست راست خود را به چکش عمله. و به چکش سیسرا را زده، سرش را سفت. و شقیقه او را شکافت و فرودوخت.۲۶
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
نزد پایهایش خم شده، افتاد و دراز شد. نزدپایهایش خم شده، افتاد. جایی که خم شد درآنجا کشته افتاد.۲۷
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
از دریچه نگریست و نعره زد، مادر سیسرا از شبکه (نعره زد): چرا ارابه‌اش در‌آمدن تاخیرمی کند؟ و چرا چرخهای ارابه هایش توقف می‌نماید؟۲۸
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
خاتونهای دانشمندش در جواب وی گفتند. لیکن او سخنان خود را به خود تکرار کرد.۲۹
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
آیا غنیمت را نیافته، و تقسیم نمی کنند؟ یک دختر دو دختر برای هر مرد. و برای سیسراغنیمت رختهای رنگارنگ، غنیمت رختهای رنگارنگ قلابدوزی، رخت رنگارنگ قلابدوزی دورو. بر گردنهای اسیران.۳۰
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
همچنین‌ای خداوند جمیع دشمنانت هلاک شوند. و اما محبان او مثل آفتاب باشند، وقتی که در قوتش طلوع می‌کند.» و زمین چهل سال آرامی یافت.۳۱

< Mahukunta 5 >