< Mahukunta 5 >
1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
Ngalolosuku uDibhora loBharakhi indodana ka-Abhinowami bahlabela ingoma le:
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
“Lapho amakhosana ko-Israyeli esekhokhela, lapho abantu bezinikela ngokuzithandela, dumisani uThixo!
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Zwanini lokhu lina makhosi! Lalelani lina babusi! Ngizahlabelela kuThixo, ngizahlabelela; ngizahubela ihubo, kuThixouNkulunkulu ka-Israyeli.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
Awu Thixo, ekuqhamukeni kwakho eSeyiri, lapho usuka elizweni lase-Edomi, umhlaba wanyikinyeka, amazulu athululeka, amayezi athululela amanzi phansi.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Izintaba zazamazama phambi kukaThixo, yena owaseSinayi, phambi kukaThixo, uNkulunkulu ka-Israyeli.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
Ensukwini zikaShamigari indodana ka-Anathi, ensukwini zikaJayeli, imigwaqo yayideliwe; izihambi zithatha izindledlana ezimazombe.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
Izakhamizi zako-Israyeli kazizange zilwe, zahlehlela emuva kwaze kwavela mina Dibhora, kwavela umama ko-Israyeli.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
UNkulunkulu wakhetha abakhokheli abatsha lapho impi isifike emasangweni edolobho, kodwa akulahawu kumbe umkhonto owabonakalayo phakathi kwezinkulungwane ezingamatshumi amane ko-Israyeli.
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
Inhliziyo yami ikanye lamakhosana ako-Israyeli, kanye labazinikela ngokuzithandela phakathi kwabantu. Dumisani uThixo!
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
Lina eligada obabhemi abamhlophe, lihlezi ezihlalweni zenu zengubo, lani elihamba emgwaqweni cabangani
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
ilizwi labahlabeleli ezindaweni zamanzi okunathisa. Bahuba ngokulunga kukaThixo, ukunqoba kwezakhamizi zako-Israyeli. Lapho-ke abantu bakaThixo behlela emasangweni edolobho.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
‘Vuka, vuka, Dibhora! Vuka, vuka, uhlabele ingoma! Vuka weBharakhi! Uthumbe abathunjiweyo bakho, wena ndodana ka-Abhinowami.’
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
Ngakho abantu ababesele bafika ezikhulwini; abantu bakaThixo beza kimi labalamandla.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
Abanye bavela ko-Efrayimi, abamdabuko wabo use-Amaleki; uBhenjamini wayelabantu abakulandelayo. Izinduna zamabutho zavela eMakhiri, koZebhuluni labo abaphatha intonga yomlawuli webutho.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
Amakhosana ako-Isakhari ayeloDibhora; yebo, u-Isakhari wayeloBharakhi emxhuma ngesiqubu ezigodini. Eziqintini zakoRubheni kwaba lokuhlolwa okukhulu kwezinhliziyo.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Lahlalelani ezibayeni ukuzwa amakhwelo enqanda izimvu na? Eziqintini zakoRubheni, kwaba lokuhlolwa okukhulu kwezinhliziyo.
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
UGiliyadi wahlala ngaphetsheya kweJodani. LoDani wasalelani ngasemikhunjini na? U-Asheri wasala ngasokhunjini wahlala emathekwini akhe olwandle.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Abantu bakoZebhuluni bafaka impilo yabo uqobo engozini; wenza njalo loNafithali emiqolweni yeganga.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
Amakhosi afika, alwa; amakhosi aseKhenani alwa, eThanakhi ngasemachibini aseMegido, kodwa kawazathwala isiliva, lempango.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
Izinkanyezi zalwa zisemazulwini, zalwa loSisera zisezindleleni zazo.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
Umfula uKhishoni wabakhukhula, umfula wendulo, umfula uKhishoni. Phambili, mphefumulo wami; Qina!
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
Kwaduma amasondo amabhiza ematha, ematha ehamba amabhiza akhe alamandla.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
‘Iqalekiseni iMerozi,’ kwatsho ingilosi kaThixo, ‘Baqalekiseni kabuhlungu abantu bayo, ngoba kabezanga ukuzencedisa uThixo, ukuzasiza uThixo emelane labalamandla.’
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Kabe ngobusiswe kakhulu kwabesifazane uJayeli, umkaHebheri umKheni, obusiswe kakhulu kwabesifazane abahlala emathenteni.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
Wacela amanzi, yena wamnika uchago, wamlethela amasi ngomganu ofanele izikhulu.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
Wathatha isikhonkwane sethente ngesandla sakhe, isandla sakhe sokudla sathatha isando somkhandi. Watshaya uSisera, wachoboza ikhanda lakhe, waphahaza wabhoboza inhlafuno yakhe.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
Wawohlokela ezinyaweni zakhe, wawa; wabhazalala khonapho. Wawohlokela ezinyaweni zakhe wawa; lapho awohlokela khona, wawela khonapho esefile.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
UnakaSisera walunguza ngefasitela; ngemva kwewindi wanqolonga wathi, ‘Kungani inqola yakhe yempi iphuze kangaka ukufika? Kungani ukugodlozela kwezinqola zakhe zempi kuphuzile?’
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
Ohlakaniphe kakhulu kumakhosazana akhe wamphendula; impela yena uhlezi ezitshela esithi,
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
‘Kanti kabafumani mpango bayabelane na; intombazana loba amabili indoda nganye, izigqoko ezimibalabala eziyimpango kaSisera, izigqoko ezimibalabala ezicecisiweyo, izigqoko eziceciswe kakhulu zentamo yami, konke lokhu kuyimpango?’
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
Ngakho sengathi zingabhubha zonke izitha zakho, Oh Thixo! Kodwa sengathi labo abakuthandayo bangaba njengelanga lapho liphuma ngamandla alo.” Kwasekusiba lokuthula elizweni iminyaka engamatshumi amane.