< Mahukunta 5 >

1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
Ce jour-là, Déborah et Barak, fils d'Abinoam, chantèrent, en disant,
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
« Parce que les dirigeants ont pris la tête en Israël, parce que le peuple s'est offert de plein gré, sois béni, Yahvé!
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
« Écoutez, vous, les rois! Écoutez, princes! Moi, même moi, je chanterai à Yahvé. Je chanterai les louanges de Yahvé, le Dieu d'Israël.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
« Yahvé, quand tu es sorti de Séir, quand vous avez marché hors du champ d'Édom, la terre a tremblé, le ciel aussi. Oui, les nuages ont laissé tomber de l'eau.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Les montagnes tremblaient devant la présence de Yahvé, même le Sinaï en présence de Yahvé, le Dieu d'Israël.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
« Au temps de Shamgar, fils d'Anath, à l'époque de Jaël, les routes étaient inoccupées. Les voyageurs marchaient dans des chemins de traverse.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
Les chefs ont cessé d'exister en Israël. Ils ont cessé jusqu'à ce que moi, Deborah, je me lève; Jusqu'à ce que je devienne une mère en Israël.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
Ils ont choisi de nouveaux dieux. Puis la guerre était aux portes. A-t-on vu un bouclier ou une lance parmi quarante mille personnes en Israël?
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
Mon cœur se tourne vers les gouverneurs d'Israël, qui se sont offerts volontairement parmi le peuple. Bénissez Yahvé!
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
« Parlez, vous qui montez des ânes blancs, vous qui êtes assis sur de riches tapis, et vous qui marchez sur le chemin.
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
Loin du bruit des archers, dans les lieux où l'on puise l'eau, ils y répéteront les actes justes de Yahvé, les actes justes de son règne en Israël. « Alors le peuple de Yahvé descendit aux portes.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
« Réveille-toi, réveille-toi, Déborah! Réveillez-vous, réveillez-vous, chantez une chanson! Lève-toi, Barak, et emmène tes captifs, fils d'Abinoam.
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
« Alors un reste des nobles et du peuple descendit. Yahvé est descendu pour moi contre les puissants.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
Ceux dont la racine est en Amalek sont sortis d'Ephraïm, après toi, Benjamin, parmi tes peuples. Les gouverneurs descendent de Machir. Ceux qui manient le bâton du maréchal sont venus de Zabulon.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
Les princes d'Issachar étaient avec Déborah. Comme Issachar, Barak l'était aussi. Ils se sont précipités dans la vallée à ses pieds. Par les cours d'eau de Reuben, il y avait de grandes résolutions de cœur.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Pourquoi vous êtes-vous assis parmi les bergeries? Pour entendre le sifflement des troupeaux? Aux cours d'eau de Reuben, il y avait de grandes recherches dans le cœur.
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Galaad vivait au-delà du Jourdain. Pourquoi Dan est-il resté dans les navires? Asher s'est assis tranquillement au bord de la mer, et vivait près de ses ruisseaux.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Zabulon était un peuple qui mettait sa vie en danger jusqu'à la mort; Nephtali aussi, sur les hauts lieux des champs.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
« Les rois sont venus et ont combattu, puis les rois de Canaan ont combattu à Taanach, près des eaux de Megiddo. Ils n'ont pas pris de butin en argent.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
Du ciel, les étoiles se sont battues. A partir de leurs cours, ils ont combattu Sisera.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
Le fleuve Kishon les a emportés, cette ancienne rivière, la rivière Kishon. Mon âme, marche avec force.
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
Alors les sabots des chevaux claquèrent à cause des cabrioles, le cabriolage de leurs forts.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
« Maudissez Méroz », dit l'ange de Yahvé. « Maudissez amèrement ses habitants, parce qu'ils ne sont pas venus pour aider Yahvé, pour aider Yahvé contre les puissants.
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
« Jaël sera béni par-dessus les femmes, l'épouse de Héber le Kenite; Elle sera bénie par rapport aux femmes de la tente.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
Il a demandé de l'eau. Elle lui a donné du lait. Elle lui a apporté du beurre dans un plat seigneurial.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
Elle a mis sa main sur le piquet de la tente, et sa main droite au marteau de l'ouvrier. Avec le marteau, elle a frappé Sisera. Elle a frappé à travers sa tête. Oui, elle a percé et frappé à travers ses tempes.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
A ses pieds, il s'est incliné, il est tombé, il s'est couché. A ses pieds, il s'est incliné, il est tombé. Là où il s'est incliné, il est tombé raide mort.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
« Par la fenêtre, elle regarda dehors et cria: La mère de Sisera a regardé à travers le treillis. Pourquoi son char tarde-t-il à venir? Pourquoi les roues de ses chars attendent-elles?
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
Ses dames sages lui répondirent, Oui, elle s'est répondu à elle-même,
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
« N'ont-ils pas trouvé, n'ont-ils pas partagé le butin? Une dame, deux dames pour chaque homme; à Sisera un butin de vêtements teints, un butin de vêtements teints et brodés, de vêtements teints brodés des deux côtés, sur le cou du butin?
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
« Que tous tes ennemis périssent donc, Yahvé, mais que ceux qui l'aiment soient comme le soleil quand il se lève dans sa force. » Ensuite, le pays s'est reposé pendant quarante ans.

< Mahukunta 5 >