< Mahukunta 5 >

1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
And Delbora and Barach, sone of Abynoen, sungen in that dai, and seiden,
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
Ye men of Israel, that `offriden wilfuli youre lyues to perel, blesse the Lord.
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Ye kingis, here, ye princes, perceyueth with eeris; Y am, Y am the womman, that schal synge to the Lord; Y schal synge to the Lord God of Israel.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
Lord, whanne thou yedist out fro Seir, and passidist bi the cuntrees of Edom, the erthe was moued, and heuenes and cloudis droppiden with watris; hillis flowiden fro the `face of the Lord,
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
and Synai fro the face of the Lord God of Israel.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
In the daies of Sangar, sone of Anach, in the daies of Jahel, paththis restiden, and thei that entriden bi tho yeden bi paththis out of the weie.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
Stronge men in Israel cessiden, and restiden, til Delbora roos, a modir in Israel.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
The Lord chees newe batels, and he destriede the yatis of enemyes; scheeld and spere apperiden not in fourti thousynde of Israel.
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
Myn herte loueth the princes of Israel; ye that offriden you to perel bi youre owyn wille,
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
blesse ye the Lord; speke ye, that stien on schynynge assis, and sitten aboue in doom, and goen in the wey.
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
Where the charis weren hurtlid doun to gidere, and the oost of enemyes was straunglid, there the `riytfulnessis of the Lord be teld, and mercy among the stronge of Israel; thanne the `puple of the Lord cam doun to the yatis, and gat prinsehod.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
Rise, rise thou, Delbora, rise thou, and speke a song; rise thou, Barach, and thou, sone of Abynoen, take thi prisoneris.
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
The relikis of the puple ben sauyd; the Lord fauyt ayens stronge men of Effraym.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
He dide awei hem in Amalech, and aftir hym of Beniamyn in to thi puplis, thou Amalech. Princes of Machir and of Zabulon yeden doun, that ledden oost to fiyte.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
The duykis of Isachar weren with Delbora, and sueden the steppis of Barach, which yaf hym silf to perel, as in to a dich, and in to helle. While Ruben was departid ayens hym silf; the strijf of greet hertyd men was foundun.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Whi dwellist thou bitwixe `tweyne endis, that thou here the hissyngis of flockis? While Ruben was departid ayens hym silf, the strijf of greet hertid men was foundun.
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Gad restide biyendis Jordan, and Dan yaf tent to schippis. Aser dwellide in the `brenke of the see, and dwellide in hauenes.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Forsothe Zabulon and Neptalym offriden her lyues to deeth, in the cuntre of Morema, `that is interpretid, hiy.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
Kyngis camen, and fouyten; kyngis of Canaan fouyten in Thanath, bisidis the watris of Magedon; and netheles thei token no thing bi prey.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
Fro heuene `me fauyt ayens hem; sterris dwelliden in her ordre and cours, and fouyten ayens Sisara.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
The stronde of Cyson drow `the deed bodies of hem, the stronde of Cadymyn, the stronde of Cyson. My soule, to-trede thou stronge men.
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
The hors howis felden, while the strongeste of enemyes fledden with bire, and felden heedli.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
Curse ye the lond of Meroth, seide the `aungel of the Lord, curse ye `the dwelleris of hym, for thei camen not to the help of the Lord, `in to the help of the strongeste of hym.
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Blessyd among wymmen be Jahel, the wijf of Aber Cyney; blessid be sche in hir tabernacle.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
To Sisara axynge watir sche yaf mylk, and in a viol of princes sche yaf botere.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
Sche puttide the left hond to a nail, and the riyt hond to the `hameris of smyythis; and sche smoot Sisara, and souyte in the heed a place of wounde, and perside strongli the temple.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
He felde bitwixe `the feet of hir, he failide, and diede; he was waltryd bifor hir feet, and he lay with out soule, and wretchidful.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
His modir bihelde bi a wyndow, and yellide; and sche spak fro the soler, Whi tarieth his chaar to come ayen? Whi tarieden the feet of his foure horsid cartis?
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
Oon wisere than `othere wyues of hym answeride these wordis to the modir of hir hosebonde,
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
In hap now he departith spuylis, and the faireste of wymmen is chosun to hym; clothis of dyuerse colouris ben youun to Sisara in to prey, and dyuerse aray of houshold is gaderid to ourne neckis.
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
Lord, alle thin enemyes perische so; sotheli, thei that louen thee, schyne so, as the sunne schyneth in his risyng. And the lond restide fourti yeer.

< Mahukunta 5 >