< Mahukunta 5 >
1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
On that day Deborah and Barak son of Abinoam sang this song:
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
“When the leaders take the lead in Israel, when the people gladly volunteer for war— we praise Yahweh!
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Listen, you kings! Pay attention, you leaders! I, I will sing to Yahweh; I will sing praises to Yahweh, the God of Israel.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
Yahweh, when you went out from Seir, when you marched from Edom, the earth shook, and the skies also trembled; also the clouds poured down water.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
The mountains quaked before the face of Yahweh; even Mount Sinai quaked before the face of Yahweh, the God of Israel.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
In the days of Shamgar (son of Anath), in the days of Jael, the main roads were abandoned, and those who walked only used the winding paths.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
There were few rural people in Israel, until I, Deborah, arose—arose as a mother in Israel!
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
When they chose new gods, there was fighting at the city gates and yet there were no shields or spears seen among forty thousand in Israel.
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
My heart goes out to the commanders of Israel, along with the people who gladly volunteered— we bless Yahweh for them!
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
Think about this—you who ride on white donkeys sitting on rugs for saddles, and you who walk along the road.
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
Hear the voices of those who sing at the watering places. There they tell again of Yahweh's righteous deeds, and the righteous actions of his warriors in Israel. Then the people of Yahweh went down to the city gates.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
Awake, awake, Deborah! Awake, awake, sing a song! Get up, Barak, and capture your prisoners, you son of Abinoam.
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
Then the survivors came down to the nobles; the people of Yahweh came down to me with the warriors.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
They came from Ephraim, whose root is in Amalek; the people of Benjamin followed you. From Machir commanders came down, and from Zebulun those who carry an officer's staff.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
My princes in Issachar were with Deborah; and Issachar was with Barak rushing after him into the valley under his command. Among the clans of Reuben there were great searchings of heart.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Why did you sit between the fireplaces, listening to the shepherds playing their pipes for their flocks? As for the clans of Reuben there were great searchings of heart.
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Gilead stayed on the other side of the Jordan; and Dan, why did he wander about on ships? Asher remained on the coast and lived close to his harbors.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Zebulun was a tribe who would risk their lives to the point of death, and Naphtali, also, on the field of battle.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
The kings came, they fought; the kings of Canaan fought at Taanach by the waters of Megiddo. But they took away no silver as plunder.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
From heaven the stars fought, from their paths across the heavens they fought against Sisera.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
The Kishon River swept them away, that old river, the Kishon River. March on my soul, be strong!
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
Then came the sound of horses' hooves— galloping, the galloping of his mighty ones.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
'Curse Meroz!' says the angel of Yahweh. 'Surely curse its inhabitants!— because they did not come to help Yahweh— to help Yahweh in the battle against the mighty warriors.'
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Jael is blessed more than all other women, Jael (the wife of Heber the Kenite), she is more blessed than all the women who live in tents.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
The man asked for water, and she gave him milk; she brought him butter in a dish fit for princes.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
She put her hand to the tent peg, and her right hand to the workman's hammer; with the hammer she struck Sisera, she crushed his head. She smashed his skull into pieces when she pierced him through the side of his head.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
He collapsed between her feet, he fell and he lay there. Between her feet he fell limp. The place he collapsed is where he was violently killed.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
Out of a window she looked— the mother of Sisera looked through the lattice and she called out in sadness, 'Why has it taken his chariot so long to come? Why have the hoofbeats of the horses that pull his chariots been delayed?'
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
Her wisest princesses replied, and she gave herself the same answer:
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
'Have they not found and divided up the plunder? —A womb, two wombs for every man; the plunder of dyed fabric for Sisera, the plunder of dyed fabric embroidered, two pieces of dyed fabric embroidered for the necks of those who plunder?'
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
So may all your enemies perish, Yahweh! But your friends be like the sun when it rises in its might.” Then the land had peace for forty years.