< Mahukunta 5 >

1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
And Deborah sings—also Barak son of Abinoam—on that day, saying,
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
“For freeing leaders in Israel, For a people willingly offering themselves, Bless YHWH.
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Hear, you kings; give ear, you princes, I sing to YHWH, I sing praise to YHWH, God of Israel.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
YHWH, in Your going forth out of Seir, In Your stepping out of the field of Edom, The earth trembled and the heavens dropped, And thick clouds dropped water.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Hills flowed from the face of YHWH, This one—Sinai—From the face of YHWH, God of Israel.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
In the days of Shamgar son of Anath—In the days of Jael—The ways have ceased, And those going in the paths go [in] crooked ways.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
Villages ceased in Israel—they ceased, Until I arose—Deborah, That I arose, a mother in Israel.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
He chooses new gods, Then war [is] at the gates! A shield is not seen—and a spear Among forty thousand in Israel.
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
My heart [is] to the lawgivers of Israel, Who are offering themselves willingly among the people, Bless YHWH!
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
Riders on white donkeys—Sitters on a long robe—And walkers by the way—meditate!
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
By the voice of shouters Between the places of drawing water, There they give out righteous acts of YHWH, Righteous acts of His villages in Israel, Then the people of YHWH have gone down to the gates.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
Awake, awake, Deborah; Awake, awake, utter a song; Rise, Barak, and take your captivity captive, Son of Abinoam.
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
Then him who is left of the majestic ones He caused to rule the people of YHWH, He caused me to rule among the mighty.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
From Ephraim [are] those whose root [is] in Amalek, After you, Benjamin, among your peoples, From Machir lawgivers came down, And from Zebulun those drawing with the reed of a writer.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
And princes in Issachar [are] with Deborah, Indeed, Issachar [is] right with Barak, Into the valley he was sent on his feet. In the divisions of Reuben, The decrees of heart [are] great!
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Why have you abided between the boundaries, To hear lowings of herds? For the divisions of Reuben, The searchings of heart [are] great!
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Gilead dwelt beyond the Jordan, And why does Dan sojourn [in] ships? Asher has abided at the haven of the seas, And dwells by his creeks.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Zebulun [is] a people who exposed its soul to death, Naphtali also—on high places of the field.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
Kings came—they fought; Then kings of Canaan fought, In Taanach, by the waters of Megiddo; They did not take gain of money!
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
They fought from the heavens: The stars fought with Sisera from their highways.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
The Brook of Kishon swept them away, The most ancient brook—the Brook of Kishon. You tread down strength, O my soul!
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
Then the horse-heels were broken, By gallopings—gallopings of its mighty ones.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
Curse Meroz, said a messenger of YHWH, Cursing, curse its inhabitants! For they did not come to the help of YHWH, To the help of YHWH among the mighty!
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Above women is Jael, The wife of Heber the Kenite, She is blessed above women in the tent.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
He asked for water—she gave milk; She brought butter near in a lordly dish.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
She sends forth her hand to the pin, And her right hand to the laborers’ hammer, And she hammered Sisera—she struck his head, Indeed, she struck, and it passed through his temple.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
He bowed between her feet—He fell, he lay down; He bowed between her feet, he fell; Where he bowed, there he fell—destroyed.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
She has looked out through the window—Indeed, she cries out—the mother of Sisera, Through the lattice: Why is his chariot delaying to come? Why have the steps of his chariot tarried?
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
The wise ones, her princesses, answer her, Indeed, she returns her sayings to herself:
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
Do they not find? They apportion spoil, A female—two females—for every head, Spoil of finger-work for Sisera, Spoil of embroidered finger-work, Finger-work—a pair of embroidered things, For the necks of the spoil!
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
So do all Your enemies perish, O YHWH, And those loving Him [are] As the going out of the sun in its might!” And the land rests [for] forty years.

< Mahukunta 5 >