< Mahukunta 5 >

1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
Then sang Deborah and Barak, the son of Abinoam, on that day, saying,
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
For that leaders led in Israel, For that the people willingly offered themselves, Bless Jehovah!
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Hear, ye kings; give ear, ye princes, I, [even] I, will sing to Jehovah; I will hymn to Jehovah the God of Israel.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
Jehovah, when thou wentest forth from Seir, When thou marchedst out of the fields of Edom, The earth trembled, and the heavens dropped, Yea, the clouds dropped water.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
The mountains quaked before the face of Jehovah, That Sinai, from before Jehovah the God of Israel.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
In the days of Shamgar the son of Anath, in the days of Jael, The roads were unused, and the travellers on highways went by crooked paths.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
The villages ceased in Israel, Ceased until that I Deborah arose, That I arose a mother in Israel.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
They chose new gods; then was war in the gates: Was there a shield or spear seen among forty thousand in Israel?
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
My heart is toward the governors of Israel, who offered themselves willingly among the people. Bless Jehovah!
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
Ye that ride on white she-asses, ye that sit on carpets, and ye that walk by the way, consider.
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
Because of the voice of those who divide [the spoil] in the midst of the places of drawing water; There they rehearse the righteous acts of Jehovah, His righteous acts toward his villages in Israel. Then the people of Jehovah went down to the gates.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
Awake, awake, Deborah! awake, awake, utter a song! Arise, Barak, and lead captive thy captives, thou son of Abinoam!
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
Then come down, thou, the remnant of nobles, [as his] people; Jehovah! come down with me in the midst of the mighty ones.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
Out of Ephraim [came] those whose root was in Amalek; After thee was Benjamin among thy peoples. Out of Machir came down governors, And out of Zebulun they that handled the staff of the ruler.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
And the princes in Issachar were with Deborah; And Issachar, like Barak; They were sent into the valley at his feet. In the divisions of Reuben there were great resolves of heart!
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Why abodest thou among the sheepfolds, To hear the bleating of the flocks? In the divisions of Reuben there were great deliberations of heart!
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Gilead abode beyond Jordan; And Dan, why did he remain in ships? Asher sat on the sea-shore, And abode in his creeks.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Zebulun is a people [that] jeoparded their lives unto death, Naphtali also, on the high places of the field.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
Kings came, — they fought; Then fought the kings of Canaan; At Taanach, by the waters of Megiddo; They took no spoil of silver.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
From heaven was the fight; The stars from their courses fought with Sisera.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
The torrent of Kishon swept them away, That ancient torrent, the torrent Kishon. My soul, thou hast trodden down strength!
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
Then did the horse-hoofs clatter with the coursings, The coursings of their steeds.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
Curse Meroz, saith the Angel of Jehovah; Curse, curse the inhabitants thereof; For they came not to the help of Jehovah, To the help of Jehovah among the mighty.
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Blessed above women shall Jael the wife of Heber the Kenite be, Blessed above women in the tent!
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
He asked water, she gave milk; In the nobles' bowl she brought forth cream.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
She put her hand to the tent-pin, And her right hand to the workmen's hammer; And she smote Sisera, she struck through his head, Shattered and pierced through his temples.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
Between her feet he bowed, he fell, he lay down: Between her feet he bowed, he fell; Where he bowed, there he fell, overcome.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
Them other of Sisera looketh out at the window, And crieth through the lattice, Why is his chariot so long in coming? Why tarry the trampings of his chariots?
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
The wise amongst her ladies answer [her], Yea, she returneth answer to herself,
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
Have they not found, divided the booty, A damsel, two damsels, to each? A booty of dyed stuffs for Sisera, A booty of dyed stuffs of embroidery, Dyed stuff of double embroidery for the neck of a spoiler?
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
So let all thine enemies perish, Jehovah! But let them that love him be as the rising of the sun in its might. And the land had rest forty years.

< Mahukunta 5 >