< Mahukunta 5 >

1 A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
Da sang Debora og Barak, Abinoams Søn, paa den Dag og sagde:
2 “Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
Lover Herren, fordi der er taget Hævn i Israel, der Folket var villigt dertil.
3 “Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Hører, I Konger! mærker, I Fyrster! jeg vil synge for Herren; Herren, Israels Gud, vil jeg lovsynge.
4 “Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
Herre! der du uddrog fra Seir, der du gik frem fra Edoms Mark, da bævede Jorden, ogsaa Himlene dryppede, ja Skyerne dryppede med Vand.
5 Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Bjergene fløde hen for Herrens Ansigt, Sinai selv, for Herrens, Israels Guds, Ansigt.
6 “A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
I Samgars, Anaths Søns, Dage, i Jaels Dage vare Stierne tomme; og de vejfarende gik ad krogede Stier.
7 Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
Landsbyerne i Israel vare tomme, de vare tomme, indtil jeg Debora stod frem, indtil jeg stod frem, en Moder i Israel.
8 Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
Da man udvalgte nye Guder, da var der Krig i Portene; der blev ikke set Skjold eller Spyd iblandt fyrretyve Tusinde i Israel.
9 Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
Mit Hjerte slaar for Israels Høvdinger, de som beviste sig villige iblandt Folket; lover Herren!
10 “Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
I, som ride paa hvide Aseninder, I, som sidde paa Tæpper, og I, som gaa paa Vejen, taler frit!
11 da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
Skytternes Bøst lyder fra de Steder, hvor man drager Vand, der prise de Herrens Retfærdighed, Retfærdighed imod hans Landsbyer i Israel. Da steg Herrens Folk ned til Portene.
12 ‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
Vaagn op, vaagn op, Debora, vaagn op, vaagn op, istem en Sang! gør dig rede, Barak, og før dine Fanger fangne bort, du Abinoams Søn!
13 “Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
Da drog en Levning af de herlige, af Folket ned; Herren drog ned for mig blandt de vældige.
14 Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
De af Efraim, som havde Bod i Amalek, stege ned efter dig Benjamin med dine Folk; af Makir nedstege Høvdinger og af Sebulon de, som føre Herskerstaven.
15 ’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
Ogsaa var der Fyrster af Isaskar med Debora, og som Isaskar saa Barak, i Dalen styrtede han frem! Ved Rubens Vandbække vare Hjertets Betænkninger store.
16 Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
Hvorfor blev du imellem Faarestierne, at høre paa Hyrdefløjten? medens Ruben blev ved sine Vandbække, var der store Ransagninger i Hjertet.
17 Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
Gilead blev boende paa hin Side Jordanen; og hvorfor blev Dan ved Skibene? Aser blev ved Havets Bred og blev boende ved sine Havbugter.
18 Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
Sebulon var et Folk, som agtede sit Liv ringe indtil Døden, i lige Maade Nafthali, paa Markens høje Steder.
19 “Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
Kongerne kom, de strede; da strede Kanaans Konger udi Thaanak ved Megiddo Vand; de fik ingen Vinding af Sølv.
20 Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
Fra Himmelen stredes der; Stjernerne fra deres høje Baner strede mod Sisera.
21 Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
Bækken Kison bortfejede dem, de gamles Bæk, Bækken Kison; træd frem, min Sjæl, med Styrke!
22 Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
Da trampede Hestenes Hove ved deres Heltes jagende, jagende Fart.
23 Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
Forbander Meros, sagde Herrens Engel, forbander, forbander dens Indbyggere, fordi de ikke kom Herren til Hjælp, Herren til Hjælp iblandt de vældige.
24 “Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
Velsignes skal Jael, Keniteren Hebers Hustru, fremfor Kvinderne; velsignes skal hun fremfor Kvinderne i noget Paulun.
25 Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
Han begærede Vand, hun gav Mælk; hun bar Fløde frem i de herliges Skaal.
26 Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
Sin Haand rakte hun ud efter Naglen og sin højre Haand efter Smedehammeren; og hun slog Sisera, sønderslog hans Hoved og knuste og igennemstak hans Tinding.
27 A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
Imellem hendes Fødder krummede han sig, faldt, laa; imellem hendes Fødder krummede han sig, faldt; hvor han krummede sig, der faldt han og var tilintetgjort.
28 “Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
Siseras Moder saa ud af Vinduet, og skreg overlydt igennem Sprinkelværket: Hvi tøver hans Vogn med at komme? hvi blive hans Vognhjul tilbage?
29 Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
De vise iblandt hendes Fyrstinder svarede hende, ogsaa svarede hun sig selv paa sine Ord:
30 ‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
Skulde de ikke finde, ja uddele til Bytte en Pige, to Piger for hver Mand? for Sisera brogede Klæder til Bytte, brogede, stukne Klæder til Bytte? brogede, stukne paa begge Sider om Halsen, til Bytte?
31 “Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.
Saa skulle, Herre! alle dine Fjender omkomme, men de, som elske ham, skulle være ligesom Solen, der gaar frem i sin Kraft. — Og Landet havde Ro fyrretyve Aar.

< Mahukunta 5 >