< Mahukunta 4 >
1 Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
Porém os filhos de Israel tornaram a fazer o que parecia mal aos olhos do Senhor, depois de falecer Ehud.
2 Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
E vendeu-os o Senhor em mão de Jabin, rei de Canaan, que reinava em Hazor: e Sisera era o capitão do seu exército, o qual então habitava em Haroseth dos gentios.
3 Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
Então os filhos de Israel clamaram ao Senhor, porquanto ele tinha novecentos carros ferrados, e vinte anos oprimia os filhos de Israel violentamente.
4 A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
E deborah, mulher profetiza, mulher de Lappidoth, julgava a Israel naquele tempo.
5 Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
E habitava debaixo das palmeiras de deborah, entre Rama e bethel, nas montanhas de Ephraim: e os filhos de Israel subiam a ela a juízo.
6 Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
E enviou, e chamou a Barac, filho de Abinoam de Kedes de Naphtali, e disse-lhe: Porventura o Senhor Deus de Israel não deu ordem, dizendo: vai, e attrahe gente ao monte de Tabor, e toma contigo dez mil homens dos filhos de Naphtali e dos filhos de Zebulon?
7 Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
E atrairei a ti para o ribeiro de Kison a Sisera, capitão do exército de Jabin, com os seus carros, e com a sua multidão: e o darei na tua mão.
8 Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
Então lhe disse Barac: Se fores comigo, irei: porém, se não fores comigo, não irei.
9 Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
E disse ela: Certamente irei contigo, porém não será tua a honra pelo caminho que levas; pois à mão de uma mulher o Senhor venderá a Sisera. E deborah se levantou, e partiu com Barac para Kedes
10 a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
Então Barac convocou a Zebulon e a Naphtali em Kedes, e subiu com dez mil homens após de si: e deborah subiu com ele,
11 To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
E Eber, keneu, se tinha apartado dos keneos, dos filhos de Hobab, sogro de Moisés: e tinha estendido as suas tendas até ao carvalho de Saanaim, que está junto a Kedes.
12 Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
E anunciaram a Sisera que Barac, filho de Abinoam, tinha subido ao monte de Tabor.
13 sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
E Sisera convocou todos os seus carros, novecentos carros ferrados, e todo o povo que estava com ele, desde Haroseth dos gentios até ao ribeiro de Kison.
14 Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
Então disse deborah a Barac: Levanta-te; porque este é o dia em que o Senhor tem dado a Sisera na tua mão: porventura o Senhor não saiu diante de ti? Barac pois desceu do monte de Tabor, e dez mil homens após dele.
15 Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
E o Senhor derrotou a Sisera, e a todos os seus carros, e a todo o seu exército ao fio da espada, diante de Barac: e Sisera desceu do carro, e fugiu a pé.
16 Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
E Barac os seguiu após dos carros, e após do exército, até Haroseth dos gentios: e todo o exército de Sisera caiu ao fio da espada, até não ficar um só.
17 Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
Porém Sisera fugiu a pé à tenda de Jael, mulher de Eber, keneu: porquanto havia paz entre Jabin, rei de Hazor, e a casa de Eber, keneu.
18 Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
E Jael saiu ao encontro de Sisera, e disse-lhe: Retira-te, senhor meu, retira-te a mim, não temas. Retirou-se a ela à tenda, e cobriu-o com uma coberta.
19 Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
Então ele lhe disse: Dá-me, peço-te, de beber uma pouca d'água; porque tenho sede. Então ela abriu um odre de leite, e deu-lhe de beber, e o cobriu.
20 Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
E ele lhe disse: Põe-te à porta da tenda; e há de ser que se alguém vier, e te perguntar, e disser: há aqui alguém? responde tu então: Não.
21 Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
Então Jael, mulher de heber, tomou uma estaca da tenda, e lançou mão dum martelo, e foi-se mansamente a ele, e lhe cravou a estaca na fonte, e a pregou na terra, estando ele porém carregado dum profundo sono, e já cançado; e assim morreu.
22 Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
E eis que, seguindo Barac a Sisera, Jael lhe saiu ao encontro, e disse-lhe: Vem, e mostrar-te-ei o homem que buscas. E veio a ela, e eis que Sisera jazia morto, e a estaca na fonte.
23 A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
Assim Deus naquele dia sujeitou a Jabin, rei de Canaan, diante dos filhos de Israel.
24 Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.
E continuou a mão dos filhos de Israel a proseguir e endurecer-se sobre Jabin, rei de Canaan: até que exterminaram a Jabin, rei de Canaan.