< Mahukunta 4 >

1 Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
Après qu'Éhud fut mort, les enfants d'Israël continuèrent à faire ce qui est mauvais devant l'Éternel.
2 Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
C'est pourquoi l'Éternel les livra entre les mains de Jabin, roi de Canaan, qui régnait à Hatsor. Le chef de son armée était Sisera, qui habitait à Harosheth-Goïm.
3 Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
Alors les enfants d'Israël crièrent à l'Éternel; car Jabin avait neuf cents chars de fer, et il opprimait avec beaucoup de violence les enfants d'Israël depuis vingt ans.
4 A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
En ce temps-là, Débora, prophétesse, femme de Lappidoth, jugeait Israël.
5 Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
Et elle siégeait sous le palmier de Débora entre Rama et Béthel, dans la montagne d'Éphraïm, et les enfants d'Israël montaient vers elle pour être jugés.
6 Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
Or, elle envoya appeler Barak, fils d'Abinoam, de Kédès, de Nephthali, et elle lui dit: L'Éternel, le Dieu d'Israël, n'a-t-il pas donné ce commandement: Va, dirige-toi sur le mont Thabor, et prends avec toi dix mille hommes des enfants de Nephthali et des enfants de Zabulon?
7 Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
J'attirerai vers toi, au torrent de Kisson, Sisera, chef de l'armée de Jabin, avec ses chars et la multitude de ses gens, et je le livrerai entre tes mains.
8 Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
Et Barak lui dit: Si tu viens avec moi, j'irai; mais si tu ne viens pas avec moi, je n'irai pas.
9 Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
Et elle répondit: J'irai, j'irai avec toi; mais tu n'auras point de gloire dans ton entreprise; car l'Éternel livrera Sisera entre les mains d'une femme. Débora se leva donc, et alla avec Barak à Kédès.
10 a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
Et Barak assembla Zabulon et Nephthali à Kédès; dix mille hommes marchèrent à sa suite; et Débora monta avec lui.
11 To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
Or, Héber, le Kénien, s'étant séparé des Kéniens, enfants de Hobab, parent de Moïse, avait dressé ses tentes jusqu'au chêne de Tsaanaïm, qui est auprès de Kédès.
12 Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
On rapporta donc à Sisera que Barak, fils d'Abinoam, était monté à la montagne de Thabor.
13 sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
Et Sisera assembla tous ses chars, neuf cents chars de fer, et tout le peuple qui était avec lui, depuis Harosheth-Goïm jusqu'au torrent de Kisson.
14 Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
Et Débora dit à Barak: Lève-toi; car voici le jour où l'Éternel a livré Sisera entre tes mains. L'Éternel ne marche-t-il pas devant toi? Et Barak descendit du mont Thabor, ayant dix mille hommes à sa suite.
15 Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
Et l'Éternel mit en déroute Sisera, et tous les chars, et tout le camp, et il les fit passer au fil de l'épée devant Barak; et Sisera descendit de son char, et s'enfuit à pied.
16 Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
Et Barak poursuivit les chars et le camp jusqu'à Harosheth-Goïm, et tout le camp de Sisera fut passé au fil de l'épée; il n'en resta pas un homme.
17 Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
Et Sisera s'enfuit à pied vers la tente de Jaël, femme de Héber, le Kénien; car il y avait paix entre Jabin, roi de Hatsor, et la maison de Héber, Kénien.
18 Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
Et Jaël sortit au-devant de Sisera, et lui dit: Entre mon seigneur, entre chez moi; ne crains point. Il entra donc chez elle dans la tente, et elle le cacha sous une couverture.
19 Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
Puis il lui dit: Je te prie, donne-moi un peu d'eau à boire, car j'ai soif. Et elle ouvrit l'outre du lait, lui donna à boire, et le couvrit.
20 Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
Il lui dit encore: Tiens-toi à l'entrée de la tente, et si l'on vient t'interroger, en disant: Y a-t-il ici quelqu'un? Tu répondras: Non.
21 Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
Mais Jaël, femme de Héber, saisit un clou de la tente; et, prenant en main le marteau, elle vint à lui doucement, et lui transperça la tempe avec ce clou, qui s'enfonça en terre. Il était profondément endormi et accablé de fatigue; et il mourut.
22 Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
Et voici, Barak poursuivait Sisera, et Jaël sortit au-devant de lui, et lui dit: Viens, et je te montrerai l'homme que tu cherches. Et Barak entra chez elle, et voici, Sisera était étendu mort, le clou dans la tempe.
23 A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
En ce jour-là, Dieu humilia ainsi Jabin, roi de Canaan, devant les enfants d'Israël.
24 Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.
Et la main des enfants d'Israël s'appesantit de plus en plus sur Jabin, roi de Canaan, jusqu'à ce qu'ils eussent exterminé Jabin, roi de Canaan.

< Mahukunta 4 >