< Mahukunta 4 >

1 Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
Mais, les fils d'Israël recommencèrent à faire le mal devant le Seigneur, et Aod était mort.
2 Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
Le Seigneur alors livra les fils d'Israël aux mains de Jabin, roi de Chanaan, qui régnait en Asor; le général de son armée était Sisara, et celui- ci demeurait en Arisoth des gentils.
3 Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
Et les fils d'Israël crièrent au Seigneur, parce que ce roi avait neuf cents chars armés de faux, et que depuis vingt ans il opprimait cruellement Israël.
4 A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
En ce temps-là, Débora, prophétesse, femme de Lapidoth, jugeait Israël.
5 Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
Elle siégeait sous le palmier de Débora, entre Rhama et Béthel, dans les montagnes d'Ephraïm; et les fils d'Israël venaient à elle pour être jugés.
6 Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
Débora envoya chercher Barac, fils d'Abinéem, de Cadès en Nephthali, et elle lui dit: Le Seigneur ne t'a-t-il pas donné ces ordres: Tu t'en iras au mont Thabor; tu prendras avec toi dix mille hommes des fils de Nephthali et des fils de Zabulon, puis,
7 Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
J'amènerai vers toi, dans le torrent de Cison, Sisara, général de l'armée de Jabin, et ses chars, et ses troupes, et je le livrerai à tes mains?
8 Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
A quoi Barac répondit: Si tu pars avec moi, je partirai; sinon, je ne partirai pas: car je ne sais pas le jour où le Seigneur me favorisera de la compagnie de son ange.
9 Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
Et elle dit: Je partirai avec toi; mais sache que tu n'auras point le premier rang dans la voie où tu veux marcher; car le Seigneur livrera Sisara aux mains d'une femme. Débora se leva donc, et elle partit de Cadès avec Barac.
10 a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
Et Barac appela de Cadès le secours de Zabulon et de Nephthali; dix mille hommes le suivirent, et Débora partit avec lui.
11 To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
Or, Haber le Cinéen s'était éloigné de Caina et des fils de Jobab, allié de Moïse; et il avait dressé sa tente vers le Chêne des Ravisseurs, qui touche à Cadès.
12 Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
Quand on apprit à Sisara que Barac, fils d'Abinéem, était allé sur le mont Thabor,
13 sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
Sisara rassembla tous ses chars, ses neuf cents chars armés de faux, avec tout le peuple qui habitait comme lui Arisoth des gentils, et il les mena dans le torrent de Cison.
14 Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
Débora dit à Barac: Debout, voici le jour où le Seigneur te livre Sisara; car le Seigneur va marcher à notre tête. Et Barac descendit du mont Thabor suivi de dix mille hommes.
15 Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
Et le Seigneur frappa Sisara d'épouvante; ses chars s'embarrassèrent; tout son camp fut passé au fil de l'épée devant Barac; et Sisara descendit de son char, et il s'enfuit à pied.
16 Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
Et Barac poursuivit ses chars et les débris du camp jusqu'à Arisoth des gentils; toute l'armée de Sisara fut passée au fil de l'épée; il n'en resta pas un seul homme.
17 Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
Cependant, Sisara s'enfuit à pied dans la tente de Jaël, femme du Cinéen Haber son ami; car il y avait paix entre Jabin, roi d'Asor, et Haber le Cinéen.
18 Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
Et Jaël sortit à la rencontre de Sisara, et elle lui dit: Entre, mon seigneur, cache-toi chez moi, n'aie point de crainte. Et il se cacha chez elle dans la tente, et elle l'enveloppa d'un manteau.
19 Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
Or, Sisara lui dit: Donne-moi à boire un peu d'eau, car j'ai bien soif. Et elle lui ouvrit l'outre à lait, et elle le fit boire; puis, elle le recouvrit.
20 Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
Et Sisara lui dit: Tiens-toi devant la porte de la tente; et si quelqu'un vient à toi, et te demande: Y a-t-il ici un homme? Réponds: Il n'y en a point.
21 Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
Et Jaël, femme d'Haber, prit un des clous de la tente; elle mit un marteau dans sa main, elle s'approcha de Sisara furtivement, et elle lui enfonça dans la tempe le clou qui traversa de part en part jusqu'à terre; et l'homme, perdant connaissance, fut enveloppe de ténèbres, et il mourut.
22 Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
Bientôt Barac parut poursuivant Sisara; Jaël sortit à sa rencontre, et elle lui dit: Viens, je vais te montrer l'homme que tu cherches. Il entra auprès d'elle, et il vit Sisara étendu mort, le clou dans la tempe.
23 A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
Ainsi, le Seigneur Dieu, ce jour-là, mit en déroute le roi Jabin, devant les fils d'Israël.
24 Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.
Et la main des fils d'Israël prévalut de plus en plus contre Jabin, roi de Chanaan, jusqu'à ce qu'ils l'eussent détruit.

< Mahukunta 4 >