< Mahukunta 4 >

1 Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
Les enfants d’Israël recommencèrent à mécontenter l’Eternel, après la mort d’Ahod;
2 Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
et l’Eternel les livra au pouvoir de Jabin, roi cananéen qui régnait à Haçor, et qui avait pour général Sisara, résidant à Harochet Haggoyim.
3 Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
Les enfants d’Israël implorèrent le Seigneur; car ce roi avait neuf cents chariots de guerre, et il molestait durement, pendant vingt ans, les enfants d’Israël.
4 A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
Or Débora, une prophétesse, femme de Lappidoth, gouvernait Israël à cette époque.
5 Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
Elle siégeait au pied du "Palmier de Débora", entre Rama et Béthel, dans la montagne d’Ephraïm; et c’est à elle que les Israélites s’adressaient pour obtenir justice.
6 Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
Elle envoya quérir Barak, fils d’Abinoam, de Kédech-en-Nephtali, et lui dit: "Voici l’ordre de l’Eternel, Dieu d’Israël: Va déployer une armée sur le mont Thabor, après avoir pris, avec toi, dix mille hommes des tribus de Nephtali et de Zabulon;
7 Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
moi, je ferai avancer de ton côté, vers le torrent de Kison, Sisara, commandant de l’armée de Jabin, avec ses chariots et sa multitude, et je le livrerai en ta main."
8 Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
Barak lui répondit: "Si tu m’accompagnes, j’irai; sinon, je n’irai point."
9 Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
Elle répliqua: "Certes, j’irai avec toi; seulement, ce n’est pas à toi que reviendra l’honneur de ton entreprise, puisque c’est à une femme que l’Eternel aura livré Sisara." Et là-dessus Débora s’en alla avec Barak à Kédech.
10 a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
Barak convoqua Zabulon et Nephtali à Kédech, dix mille hommes montèrent à sa suite, et Débora monta avec lui.
11 To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
(Or, Héber, le Kénéen, s’était séparé des Kénéens, des descendants de Hobab, beau-père de Moïse; et il avait dressé sa tente vers le Chêne de Çaanannîm, qui est près de Kédech.)
12 Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
Sisara, ayant appris que Barak, fils d’Abinoam, s’était dirigé sur le mont Thabor,
13 sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
réunit tous ses chariots, neuf cents chariots armés de fer, ainsi que toute la milice sous ses ordres, et les achemina de Harochet Haggoyim vers le torrent de Kison.
14 Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
Alors Débora dit à Barak: "En avant! car c’est aujourd’hui que le Seigneur livre en tes mains Sisara; n’est-ce pas Dieu même qui marche devant toi?" Et Barak descendit du mont Thabor, suivi de dix mille hommes.
15 Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
L’Eternel frappa de perturbation Sisara, tous ses attelages et toute son armée, qu’il livra au glaive de Barak; Sisara sauta à bas de son char et s’enfuit à pied.
16 Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
Barak poursuivit attelages et armée jusqu’à Harochet Haggoyim; et toute l’armée de Sisara tomba sous le tranchant du glaive, pas un seul n’échappa.
17 Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
Cependant Sisara fuyait à pied vers la tente de Jaël, femme de Héber le Kénéen; car il y avait paix entre Jabin, roi de Haçor, et la famille de Héber le Kénéen.
18 Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
Jaël sortit à la rencontre de Sisara et lui dit: "Entre, seigneur, entre chez moi, ne crains rien!" Il la suivit dans la tente, et elle le cacha sous une couverture.
19 Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
Il lui dit: "Donne-moi, je te prie, un peu d’eau à boire, j’ai soif!" Et elle ouvrit l’outre au lait, lui donna à boire et le recouvrit.
20 Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
Il lui dit: "Tiens-toi à l’entrée de la tente, et si l’on vient te demander: Y a-t-il quelqu’un ici? tu répondras: Non.
21 Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
Or Jaël, femme de Héber, prit une cheville de la tente, se saisit d’un marteau, se glissa près de lui sans bruit et enfonça dans sa tempe la cheville, qui resta fichée en terre; lui, fatigué, s’était endormi; il mourut.
22 Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
Cependant Barak vint, poursuivant Sisara; Jaël s’avança à sa rencontre et lui dit: "Viens, je vais te faire voir l’homme que tu cherches." Il la suivit et vit Sisara étendu mort, la tempe traversée par la cheville.
23 A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
Ce jour-là, Dieu abattit Jabin, roi de Canaan, devant les enfants d’Israël;
24 Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.
et la puissance des enfants d’Israël alla s’appesantissant sur Jabin, roi de Canaan, si bien qu’ils consommèrent sa ruine.

< Mahukunta 4 >