< Mahukunta 4 >

1 Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
And the sons of Israel again did that which was evil in the sight of Jehovah, when Ehud was dead.
2 Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
And Jehovah sold them into the hand of Jabin king of Canaan who reigned in Hazor, the captain of whose army was Sisera who dwelt in Harosheth of the Gentiles.
3 Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
And the sons of Israel cried to Jehovah, for he had nine hundred chariots of iron, and he mightily oppressed the sons of Israel twenty years.
4 A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
Now Deborah, a prophetess, the wife of Lappidoth, she judged Israel at that time.
5 Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
And she dwelt under the palm tree of Deborah between Ramah and Bethel in the hill-country of Ephraim, and the sons of Israel came up to her for judgment.
6 Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
And she sent and called Barak the son of Abinoam out of Kedesh-naphtali, and said to him, Has not Jehovah, the God of Israel, commanded, saying, Go and approach to mount Tabor, and take with thee ten thousand men of the sons of Naphtali and of the sons of Zebulun?
7 Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
And I will draw Sisera, the captain of Jabin's army, to thee, to the river Kishon, with his chariots and his multitude, and I will deliver him into thy hand.
8 Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
And Barak said to her, If thou will go with me, then I will go, but if thou will not go with me, I will not go.
9 Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
And she said, I will surely go with thee. Notwithstanding, the journey that thou take shall not be for thine honor, for Jehovah will sell Sisera into the hand of a woman. And Deborah arose, and went with Barak to Kedesh.
10 a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
And Barak called Zebulun and Naphtali together to Kedesh. And there went up ten thousand men at his feet, and Deborah went up with him.
11 To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
Now Heber the Kenite had separated himself from the Kenites, even from the sons of Hobab the brother-in-law of Moses, and had pitched his tent as far as the oak in Zaanannim, which is by Kedesh.
12 Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
And they told Sisera that Barak the son of Abinoam was gone up to mount Tabor.
13 sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
And Sisera gathered together all his chariots, even nine hundred chariots of iron, and all the people that were with him, from Harosheth of the Gentiles, to the river Kishon.
14 Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
And Deborah said to Barak, Up, for this is the day in which Jehovah has delivered Sisera into thy hand. Has not Jehovah gone out before thee? So Barak went down from mount Tabor, and ten thousand men after him.
15 Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
And Jehovah discomfited Sisera, and all his chariots, and all his army, with the edge of the sword before Barak. And Sisera alighted from his chariot, and fled away on his feet.
16 Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
But Barak pursued after the chariots, and after the army, to Harosheth of the Gentiles. And all the army of Sisera fell by the edge of the sword. There was not a man left.
17 Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
However Sisera fled away on his feet to the tent of Jael the wife of Heber the Kenite, for there was peace between Jabin the king of Hazor and the house of Heber the Kenite.
18 Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
And Jael went out to meet Sisera, and said to him, Turn in, my lord, turn in to me; fear not. And he turned in to her into the tent, and she covered him with a rug.
19 Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
And he said to her, Give me, I pray thee, a little water to drink, for I am thirsty. And she opened a bottle of milk, and gave him drink, and covered him.
20 Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
And he said to her, Stand in the door of the tent, and it shall be, when any man comes and inquires of thee, and says, Is there any man here? that thou shall say, No.
21 Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
Then Jael Heber's wife took a tent-pin, and took a hammer in her hand, and went softly to him, and struck the pin into his temples, and it pierced through into the ground, for he was in a deep sleep, so he fainted and died.
22 Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
And, behold, as Barak pursued Sisera, Jael came out to meet him, and said to him, Come, and I will show thee the man whom thou seek. And he came to her, and, behold, Sisera lay dead, and the tent-pin was in his temples.
23 A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
So God subdued on that day Jabin the king of Canaan before the sons of Israel.
24 Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.
And the hand of the sons of Israel prevailed more and more against Jabin the king of Canaan until they had destroyed Jabin king of Canaan.

< Mahukunta 4 >