< Mahukunta 4 >
1 Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
Bangʼ ka Ehud nosetho, jo-Israel nochako otimo tim mamono e wangʼ Jehova Nyasaye.
2 Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
Omiyo Jehova Nyasaye nousogi ne Jabin, ruodh Kanaan, ma loch mare neni Hazor. Jatend jolweny mage ne en Sisera, manodak Harosheth Hagoyim.
3 Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
Nikech ne en-gi geche chuma mia ochiko kendo notiyo jo-Israel gachuna kuom higni piero ariyo, ne giywakne Jehova Nyasaye mondo oresgi.
4 A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
Debora, janabi madhako, ma chi Lapidoth, notelo ne jo-Israel e kindeno.
5 Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
Nobedo gi kar ngʼado bura e bwo Yadh Othith mar Debora mantiere kind Rama kod Bethel manie piny gode mar Efraim, kendo jo-Israel ne biro ire kanyo mondo ongʼadnegi bura.
6 Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
Noluongo Barak wuod Abinoam moa Kedesh man Naftali kendo owachone niya, “Jehova Nyasaye ma Nyasach Israel, chiki ni, ‘Dhiyo, ikaw ji alufu apar mag Naftali kod Zebulun kendo itelnegi ka udhi e Got Tabor.
7 Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
Abiro wuondo Sisera, jatend jolwenj Jabin, kanyakla gi gechene kod ogandage mag lweny nyaka e Aora Kishon kendo achiwe e lweti.’”
8 Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
Barak nowachone niya, “Ka idhi koda, abiro dhi; to ka ok idhi koda, to ok abi dhi.”
9 Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
Debora nowachone niya, “Mano kare, abiro dhi kodi. To nikech yo ma itimoe gini duongʼ, ok nobed mari, nimar Jehova Nyasaye nochiw Sisera ne dhako.” Omiyo Debora nodhi gi Barak nyaka Kedesh,
10 a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
kama noluonge Zebulun kod Naftali. Ji alufu apar noluwo bangʼe, kendo Debora bende nodhi kode.
11 To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
Koro Heber ja-Keni noseweyo jo-Keni ma nyikwa Hobab, ma en or Musa, kendo oguro hembe machiegni gi yien maduongʼ man Zananim but Kedesh.
12 Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
Kane ginyiso Sisera ni Barak wuod Abinoam nosedhi Got Tabor,
13 sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
Sisera nochoko kanyakla gechene mag chuma mia ochiko kod chwo duto kode, koa Harosheth Hagoyim nyaka e Aora Kishon.
14 Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
Eka Debora nowachone Barak niya, “Dhiyo! Ma e odiechiengʼ ma Jehova Nyasaye osechiwo Sisera e lweti. Donge Jehova Nyasaye osedhi nyimi?” Omiyo Barak nodhi e Got Tabor, kiluwe gi ji alufu apar.
15 Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
Kaka Barak ne sudo machiegni, Jehova Nyasaye nogoyo Sisera, jolweny mage kod gechene gi kihondko kendo Sisera nojwangʼo gache mi oringo gi tiende.
16 Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
To Barak nodhi nyime gi lawo geche kod jolweny ma ochopo Harosheth Hagoyim. Oganda lweny duto mar Sisera noneg gi ligangla; kendo onge ngʼama notony.
17 Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
Kata kamano, Sisera, noringo nyaka e hemb Jael, ma chi Heber ja-Keni, nikech ne nitie osiep e kind Jabin ruodh Hazor kod anywola Heber ja-Keni.
18 Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
Jael nowuok mondo orom gi Sisera kendo owachone niya, “Bi, ruodha, donji. Kik iluor.” Omiyo nodonjo ei hembe, kendo noume.
19 Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
Nowacho niya, “Awinjo riyo. Kiyie to miya pi amodhi.” Noyawo chupa mar chak, momiye omadho, bangʼe oume kendo.
20 Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
Nowachone niya, “Chungʼ e dhood hema. Ka ngʼato obiro kendo openji ni, ‘Bende ngʼato nitiere ka?’ To wachne ni, ‘Ooyo.’”
21 Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
Jael, ma chi Heber, nokawo sigingi mar hema kod nyundo kendo nodhi ire mapiyo kama nindo nogoye ngoga, kendo ool. Nopowo iye gi sigingino nyaka e lowo, mi otho.
22 Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
Barak nobiro kolawo Sisera, kendo Jael nowuok mondo orom kode. Nowachone niya, “Bi, abiro nyisi ngʼat ma imanyo.” Omiyo nodhi kode, kendo kanyo Sisera nonindo gi sigingi kopowo iye kosetho.
23 A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
E odiechiengno Nyasaye nomako Jabin, ruodh Kanaan, e nyim jo-Israel.
24 Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.
Chakre e kindeno Israel nobedo motegno mine giloyo Jabin ruodh Kanaan.