< Mahukunta 3 >

1 Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
A ovo su narodi koje ostavi Gospod da njima kuša Izrailja, sve one koji ne znahu za ratove Hananske,
2 (ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
Da bi barem natražje sinova Izrailjevijeh znalo i razumjelo što je rat, barem oni koji od prije nijesu znali:
3 sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
Pet kneževina Filistejskih, i svi Hananeji i Sidonci i Jeveji, koji življahu na gori Livanu od gore Val-Ermona do Emata.
4 An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
Ti narodi ostaše da se Izrailj njima kuša, da se vidi hoæe li slušati zapovijesti Gospodnje, koje je zapovjedio ocima njihovijem preko Mojsija.
5 Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
I življahu sinovi Izrailjevi usred Hananeja i Heteja i Amoreja i Ferezeja i Jeveja i Jevuseja.
6 Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
I ženjahu se kæerima njihovijem i udavahu kæeri svoje za sinove njihove, i služahu bogovima njihovijem.
7 Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
I èinjahu sinovi Izrailjevi što je zlo pred Gospodom, i zaboraviše Gospoda Boga svojega i služahu Valima i lugovima.
8 Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
Zato se razgnjevi Gospod na Izrailja, i dade ih u ruke Husan-Risatajimu caru Mesopotamskom; i služiše sinovi Izrailjevi Husan-Risatajimu osam godina.
9 Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
Potom vapiše sinovi Izrailjevi ka Gospodu, i podiže Gospod izbavitelja sinovima Izrailjevijem da ih izbavi, Gotonila sina Kenezova, mlaðega brata Halevova,
10 Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
I bijaše na njemu duh Gospodnji, i suðaše Izrailju; i izide na vojsku, i predade mu Gospod u ruke Husan-Risatajima cara Mesopotamskoga; i ruka njegova nadjaèa Husan-Risatajima.
11 Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
I zemlja bi mirna èetrdeset godina. Potom umrije Gotonilo sin Kenezov.
12 Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
A sinovi Izrailjevi stadoše opet èiniti što je zlo pred Gospodom; a Gospod ukrijepi Eglona cara Moavskoga na Izrailja, jer èinjahu što je zlo pred Gospodom.
13 Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
Jer skupi k sebi sinove Amonove i Amalike, i izašavši pobi Izrailja, i osvojiše grad palmov.
14 Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
I sinovi Izrailjevi služiše Eglonu caru Moavskom osamnaest godina.
15 Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
Potom vapiše sinovi Izrailjevi ka Gospodu; i Gospod im podiže izbavitelja Aoda sina Gire sina Venijaminova, èovjeka koji bijaše ljevak. I poslaše sinovi Izrailjevi po njemu dar Eglonu caru Moavskom.
16 To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
A Aod naèini sebi maè s obje strane oštar, od lakta u dužinu; i pripasa ga pod haljine svoje uz desnu bedricu.
17 Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
I odnese dar Eglonu caru Moavskom; a Eglon bješe èovjek vrlo debeo.
18 Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
I kad predade dar, otpusti ljude koji su nosili dar.
19 A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
Pa sam vrativ se od likova kamenijeh, koji bijahu kod Galgala, reèe: imam, care, neku tajnu da ti kažem. A on reèe: muèi! I otidoše od njega svi koji stajahu pred njim.
20 Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
A Aod pristupi k njemu; a on sjeðaše sam u ljetnoj sobi; pa reèe Aod: rijeè Božiju imam da ti kažem. Tada on usta s prijestola.
21 Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
A Aod poteže lijevom rukom svojom i uze maè od desne bedrice, i satjera mu ga u trbuh,
22 Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
I držak uðe za maèem, i salo se sklopi za maèem, te ne može izvuæi maèa iz trbuha; i izide neèist.
23 Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
Potom izide Aod iz sobe, i zatvori vrata za sobom i zakljuèa.
24 Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
A kad on otide, doðoše sluge, i pogledaše, a to vrata od sobe zakljuèana, pa rekoše: valjada ide napolje u klijeti do ljetne sobe.
25 Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
I veæ im se dosadi èekati a vrata se od sobe ne otvoraju, te uzeše kljuè i otvoriše, a gle, gospodar im leži na zemlji mrtav.
26 Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
A Aod dokle se oni zabaviše pobježe i proðe likove kamene, i uteèe u Seirot.
27 Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
I kad doðe, zatrubi u trubu u gori Jefremovoj; i sidoše s njim sinovi Izrailjevi s gore, a on naprijed.
28 Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
Pa im reèe: hajdete za mnom, jer Gospod predade vam u ruke neprijatelje vaše Moavce. I sidoše za njim, i uzeše Moavcima brodove Jordanske, i ne dadijahu nikome prijeæi.
29 A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
I tada pobiše Moavce, oko deset tisuæa ljudi, sve bogate i hrabre, i nijedan ne uteèe.
30 A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
Tako u taj dan potpadoše Moavci pod ruku Izrailjevu; i zemlja bi mirna osamdeset godina.
31 Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.
A poslije njega nasta Samegar sin Anatov, i pobi šest stotina Filisteja ostanom volujskim, i izbavi i on Izrailja.

< Mahukunta 3 >