< Mahukunta 3 >

1 Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
Or ce sont ici les nations que l'Eternel laissa pour éprouver par elles Israël, [savoir] tous ceux qui n'avaient point eu connaissance de toutes les guerres de Canaan;
2 (ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
Afin qu'au moins les générations des enfants d'Israël sussent et apprissent ce que c'est que la guerre; au moins ceux qui auparavant n'en avaient rien connu.
3 sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
[Ces nations donc furent] les cinq Gouvernements des Philistins, et tous les Cananéens, les Sidoniens, et les Héviens, qui habitaient en la montagne du Liban, depuis la montagne de Bahal-hermon, jusqu'à l'entrée de Hamath.
4 An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
[Ces nations], dis-je, servirent à éprouver Israël, pour voir s'ils obéiraient aux commandements de l'Eternel, lesquels il avait donnés à leurs pères par le moyen de Moïse.
5 Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
Ainsi les enfants d'Israël habitèrent parmi les Cananéens, les Héthiens, les Amorrhéens, les Phérésiens, les Héviens, et les Jébusiens.
6 Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
Et ils prirent leurs filles pour femmes, et ils donnèrent leurs filles à leurs fils, et servirent leurs dieux.
7 Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
Les enfants d'Israël firent donc ce qui déplaît à l'Eternel; ils oublièrent l'Eternel leur Dieu, et servirent les Bahalins, et les bocages.
8 Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
C'est pourquoi la colère de l'Eternel s'enflamma contre Israël, et il les vendit en la main de Cusan-rischathajim, Roi de Mésopotamie. Et les enfants d'Israël furent asservis à Cusan-rischathajim huit ans.
9 Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
Puis les enfants d'Israël crièrent à l'Eternel, et l'Eternel leur suscita un Libérateur qui les délivra, [savoir] Hothniël, fils de Kénas, frère puîné de Caleb.
10 Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
Et l'Esprit de l'Eternel fut sur lui, et il jugea Israël, et sortit en bataille, et l'Eternel livra entre ses mains Cusan-rischathajim, Roi d'Aram; et sa main fut fortifiée contre Cusan-rischathajim.
11 Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
Et le pays fut en repos quarante ans. Puis Hothniel, fils de Kénas, mourut.
12 Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
Et les enfants d'Israël se mirent encore à faire ce qui déplaît à l'Eternel; et l'Eternel fortifia Héglon, Roi de Moab, contre Israël, parce qu'ils avaient fait ce qui déplaît à l'Eternel.
13 Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
Et [Héglon] assembla auprès de lui les enfants d'Hammon et d'Hamalec, et il alla, et frappa Israël, et ils s'emparèrent de la ville des palmes.
14 Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
Et les enfants d'Israël furent asservis à Héglon, Roi de Moab, dix-huit ans.
15 Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
Puis les enfants d'Israël crièrent à l'Eternel, et l'Eternel leur suscita un Libérateur, [savoir] Ehud, fils de Guéra Benjamite, duquel la main droite était serrée. Et les enfants d'Israël envoyèrent par lui un présent à Héglon, Roi de Moab.
16 To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
Or Ehud s'était fait une épée à deux tranchants, de la longueur d'une coudée, qu'il avait ceinte sous ses vêtements sur sa cuisse droite.
17 Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
Et il présenta le don à Héglon, Roi de Moab; et Héglon était un homme fort gras.
18 Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
Or il arriva que quand il eut achevé de présenter le don, il reconduisit le peuple qui avait apporté le don.
19 A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
Mais [Ehud] s'en étant retourné depuis les carrières de pierre, qui [étaient] vers Guilgal, il dit: Ô Roi! j'ai à te dire quelque chose en secret. Et il lui répondit: Tais-toi, et tous ceux qui étaient auprès de lui, sortirent de là.
20 Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
Et Ehud s'approchant de lui, qui était assis seul dans sa chambre d'Eté, il lui dit: J'ai un mot à te dire de la part de Dieu. Alors [le Roi] se leva du trône.
21 Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
Et Ehud avançant sa main gauche, prit l'épée de dessus sa cuisse droite, et la lui enfonça dans le ventre;
22 Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
Et la poignée entra après la lame, et la graisse serra tellement la lame, qu'il ne pouvait tirer l'épée du ventre; et il en sortit de la fiente.
23 Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
Après cela Ehud sortit par le porche, fermant après soi les portes de la chambre, laquelle il ferma à la clef.
24 Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
Ainsi il sortit; et les serviteurs d'Héglon vinrent, et regardèrent, et voilà, les portes de la chambre étaient fermées à la clef; et ils dirent: Sans doute il est à ses affaires dans sa chambre d'Eté.
25 Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
Et ils attendirent tant qu'ils en furent honteux; et voyant qu'il n'ouvrait point les portes de la chambre, ils prirent la clef, et l'ouvrirent; et voici, leur Seigneur était étendu mort à terre.
26 Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
Mais Ehud échappa tandis qu'ils s'amusaient, et passa les carrières de pierre, et se sauva à Séhira.
27 Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
Et quand il y fut entré, il sonna de la trompette en la montagne d'Ephraïm, et les enfants d'Israël descendirent avec lui en la montagne; et il marchait devant eux.
28 Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
Et il leur dit: Suivez-moi, car l'Eternel a livré entre vos mains les Moabites vos ennemis. Ainsi ils descendirent après lui, et se saisissant des passages du Jourdain contre les Moabites, ils ne laissèrent passer personne.
29 A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
Et en ce temps-là ils frappèrent des Moabites environ dix mille hommes, tous en bon état, et tous vaillants, et il n'en échappa aucun.
30 A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
En ce jour-là donc Moab fut humilié sous la main d'Israël; et le pays fut en repos quatre-vingts ans.
31 Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.
Et après lui fut [en sa place] Samgar, fils d'Hanath, qui frappa six cents Philistins avec un aiguillon à bœufs, et qui délivra Israël.

< Mahukunta 3 >