< Mahukunta 3 >

1 Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
Voici les nations que l'Éternel laissa pour mettre Israël à l'épreuve par elles, tous ceux qui n'avaient pas connu toutes les guerres de Canaan,
2 (ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
afin que les générations des enfants d'Israël le sachent, pour leur apprendre la guerre, du moins à ceux qui ne l'avaient pas connue auparavant:
3 sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
les cinq princes des Philistins, tous les Cananéens, les Sidoniens et les Héviens qui habitaient la montagne du Liban, depuis la montagne de Baal Hermon jusqu'à l'entrée de Hamath.
4 An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
On les laissa pour éprouver Israël par eux, afin de savoir s'ils écouteraient les commandements de l'Éternel, qu'il avait prescrits à leurs pères par Moïse.
5 Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
Les enfants d'Israël habitaient parmi les Cananéens, les Hittites, les Amorites, les Perizzites, les Hivvites et les Jébusites.
6 Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
Ils prirent leurs filles pour femmes, donnèrent leurs propres filles à leurs fils et servirent leurs dieux.
7 Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
Les enfants d'Israël firent ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, ils oublièrent l'Éternel, leur Dieu, et servirent les Baals et les Ashéroths.
8 Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
La colère de l'Éternel s'enflamma contre Israël, et il les vendit entre les mains de Cushan Rishathaim, roi de Mésopotamie; les enfants d'Israël furent au service de Cushan Rishathaim pendant huit ans.
9 Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
Lorsque les enfants d'Israël crièrent à l'Éternel, l'Éternel suscita aux enfants d'Israël un sauveur qui les sauva, Othniel, fils de Kenaz, frère cadet de Caleb.
10 Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
L'Esprit de Yahvé descendit sur lui, et il jugea Israël. Il partit en guerre, et Yahvé livra entre ses mains Cushan Rishathaim, roi de Mésopotamie. Sa main l'emporta sur Cushan Rishathaim.
11 Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
Le pays fut en repos pendant quarante ans, puis Othniel, fils de Kenaz, mourut.
12 Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
Les enfants d'Israël firent encore ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, et l'Éternel fortifia Églon, roi de Moab, contre Israël, parce qu'ils avaient fait ce qui est mal aux yeux de l'Éternel.
13 Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
Il rassembla à lui les fils d'Ammon et d'Amalek, et il alla frapper Israël, et ils possédèrent la ville des palmiers.
14 Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
Les enfants d'Israël servirent Églon, roi de Moab, pendant dix-huit ans.
15 Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
Mais lorsque les enfants d'Israël crièrent à Yahvé, Yahvé leur suscita un sauveur: Ehud, fils de Gera, le Benjamite, un gaucher. Les enfants d'Israël envoyèrent par lui un tribut à Eglon, roi de Moab.
16 To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
Ehud se fabriqua une épée à deux tranchants, longue d'une coudée, qu'il porta sous ses vêtements, sur sa cuisse droite.
17 Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
Il offrit le tribut à Églon, roi de Moab. Or Églon était un homme très gras.
18 Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
Quand Ehud eut fini d'offrir le tribut, il renvoya les gens qui portaient le tribut.
19 A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
Mais lui-même s'éloigna des idoles de pierre qui se trouvaient près de Gilgal et dit: « J'ai un message secret pour toi, ô roi. » Le roi dit: « Tais-toi! » Tous ceux qui se tenaient près de lui le quittèrent.
20 Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
Ehud vint le trouver, et il était assis seul dans la chambre haute et fraîche. Ehud dit: « J'ai un message de Dieu pour toi. » Il se leva de son siège.
21 Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
Ehud étendit sa main gauche, prit l'épée de sa cuisse droite et se la planta dans le corps.
22 Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
La poignée entra aussi après la lame; et la graisse se referma sur la lame, car il n'avait pas retiré l'épée de son corps; et elle sortit par derrière.
23 Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
Ehud sortit sur le portique, ferma sur lui les portes de la chambre haute et les verrouilla.
24 Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
Après qu'il fut parti, ses serviteurs vinrent et virent que les portes de la chambre haute étaient fermées. Ils dirent: « Il est sûrement en train de se couvrir les pieds dans la chambre haute. »
25 Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
Ils attendirent jusqu'à ce qu'ils aient honte; et voici qu'il n'ouvrait pas les portes de la chambre haute. Ils prirent donc la clé et les ouvrirent, et voici que leur seigneur était tombé mort sur le sol.
26 Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
Ehud s'échappa pendant qu'ils attendaient, passa au-delà des idoles de pierre et se sauva à Seirah.
27 Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
Lorsqu'il fut arrivé, il sonna de la trompette dans la montagne d'Ephraïm; les enfants d'Israël descendirent avec lui de la montagne, et il les conduisit.
28 Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
Il leur dit: « Suivez-moi, car Yahvé a livré entre vos mains les Moabites, vos ennemis. » Ils le suivirent et prirent les gués du Jourdain contre les Moabites, et ne permirent à aucun homme de passer.
29 A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
Ils frappèrent en ce temps-là environ dix mille hommes de Moab, tous les hommes forts et tous les hommes valeureux. Aucun homme n'échappa.
30 A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
Moab fut donc soumis en ce jour sous la main d'Israël. Et le pays fut en repos pendant quatre-vingts ans.
31 Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.
Après lui, Shamgar, fils d'Anath, frappa six cents hommes des Philistins avec un aiguillon à bœuf. Il sauva aussi Israël.

< Mahukunta 3 >