< Mahukunta 3 >

1 Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
Now these [are] the nations which the LORD left, to prove Israel by them, ([even] as many [of Israel] as had not known all the wars of Canaan;
2 (ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
Only that the generations of the children of Israel might know to teach them war, at the least such as before knew nothing of it; )
3 sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
[Namely], five lords of the Philistines, and all the Canaanites, and the Sidonians, and the Hivites that dwelt on mount Lebanon, from mount Baal-hermon to the entrance of Hamath.
4 An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
And they were to prove Israel by them, to know whether they would hearken to the commandments of the LORD, which he commanded their fathers by the hand of Moses.
5 Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
And the children of Israel dwelt among the Canaanites, Hittites, and Amorites, and Perizzites, and Hivites, and Jebusites:
6 Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
And they took their daughters to be their wives, and gave their daughters to their sons, and served their gods.
7 Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
And the children of Israel did evil in the sight of the LORD, and forgot the LORD their God, and served Baalim, and the groves.
8 Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
Therefore the anger of the LORD was hot against Israel, and he sold them into the hand of Chushan-rishathaim king of Mesopotamia: and the children of Israel served Chushan-rishathaim eight years.
9 Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
And when the children of Israel cried to the LORD, the LORD raised up a deliverer to the children of Israel, who delivered them, [even] Othniel the son of Kenaz, Caleb's younger brother.
10 Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
And the Spirit of the LORD came upon him, and he judged Israel, and went out to war: and the LORD delivered Chushan-rishathaim king of Mesopotamia into his hand; and his hand prevailed against Chushan-rishathaim.
11 Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
And the land had rest forty years: and Othniel the son of Kenaz died.
12 Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
And the children of Israel did evil again in the sight of the LORD: and the LORD strengthened Eglon the king of Moab against Israel, because they had done evil in the sight of the LORD.
13 Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
And he gathered to him the children of Ammon and Amalek, and went and smote Israel, and possessed the city of palm-trees.
14 Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
So the children of Israel served Eglon the king of Moab eighteen years.
15 Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
But when the children of Israel cried to the LORD, the LORD raised them up a deliverer, Ehud the son of Gera, a Benjaminite, a man left-handed: and by him the children of Israel sent a present to Eglon king of Moab.
16 To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
But Ehud made him a dagger which had two edges, of a cubit length; and he girded it under his raiment upon his right thigh.
17 Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
And he brought the present to Eglon king of Moab: and Eglon [was] a very fat man.
18 Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
And when he had made an end to offer the present, he sent away the people that bore the present.
19 A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
But he himself turned again from the quarries that [were] by Gilgal, and said, I have a secret errand to thee, O king: who said, Keep silence. And all that stood by him went out from him.
20 Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
And Ehud came to him; and he was sitting in a summer-parlor, which he had for himself alone: and Ehud said, I have a message from God to thee. And he arose from [his] seat.
21 Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
And Ehud put forth his left hand, and took the dagger from his right thigh, and thrust it into his belly:
22 Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
And the haft also entered after the blade: and the fat closed upon the blade, so that he could not draw the dagger out of his belly; and the dirt came out.
23 Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
Then Ehud went forth through the porch, and shut the doors of the parlor upon him, and locked them.
24 Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
When he had gone out, his servants came; and when they saw that, behold, the doors of the parlor [were] locked, they said, Surely he covereth his feet in his summer-chamber.
25 Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
And they tarried till they were ashamed: and behold, he opened not the doors of the parlor, therefore they took a key and opened [them]: and behold, their lord lay dead on the earth.
26 Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
And Ehud escaped while they tarried; and passed beyond the quarries, and escaped to Seirath.
27 Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
And it came to pass when he had come, that he blew a trumpet in the mountain of Ephraim, and the children of Israel went down with him from the mount, and he before them.
28 Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
And he said to them, Follow me: for the LORD hath delivered your enemies the Moabites into your hand. And they went down after him, and took the fords of Jordan towards Moab, and suffered not a man to pass over.
29 A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
And they slew of Moab at that time about ten thousand men, all lusty, and all men of valor: and there escaped not a man.
30 A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
So Moab was subdued that day under the hand of Israel: and the land had rest eighty years.
31 Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.
And after him was Shamgar the son of Anath, who slew of the Philistines six hundred men with an ox-goad; and he also delivered Israel.

< Mahukunta 3 >