< Mahukunta 3 >
1 Waɗannan su ne al’umman da Ubangiji ya bari don yă gwada duk waɗannan Isra’ilawan da ba su san yaƙi a Kan’ana ba
And these [are] the nations which he left Yahweh to put to [the] test by them Israel all [those] who not they had known all [the] wars of Canaan.
2 (ya yi haka ne domin yă koya wa zuriyar Isra’ilawa waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba),
Only so as to know [the] generations of [the] people of Israel to teach them war only which before not they had known them.
3 sarakuna biyar na Filistiyawa, dukan Kan’aniyawa, Sidoniyawa, da kuma Hiwiyawan da suke zaune a duwatsun Lebanon daga Dutsen Ba’al-Hermon zuwa Lebo Hamat.
[the] five - [the] rulers of [the] Philistines And all the Canaanite[s] and the Sidonian[s] and the Hivite[s] [who] dwelt of [the] mount of Lebanon from [the] mountain of Baal Hermon to Lebo Hamath.
4 An bar su domin su gwada Isra’ilawa a ga ko za su yi biyayya da umarnin Ubangiji, wanda ya ba wa kakanninsu ta wurin Musa.
And they were to put to [the] test by them Israel to know ¿ will they obey [the] commandments of Yahweh which he had commanded ancestors their by [the] hand of Moses.
5 Isra’ilawa suka zauna tare da Kan’aniyawa da Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da kuma Yebusiyawa.
And [the] people of Israel they dwelt in [the] midst of the Canaanite[s] the Hittite[s] and the Amorite[s] and the Perizzite[s] and the Hivite[s] and the Jebusite[s].
6 Suka auri’ya’yansu mata, su ma suka bar’ya’yansu maza suka auri’ya’yansu mata, suka kuma yi wa gumakansu sujada.
And they took daughters their for themselves to wives and daughters their they gave to sons their and they served gods their.
7 Isra’ilawa suka aikata mugunta a gaban Ubangiji; suka manta da Ubangiji Allahnsu suka kuma bauta wa Ba’al da Ashera.
And they did [the] people of Israel the evil in [the] eyes of Yahweh and they forgot Yahweh God their and they served the Baals and the Asherah poles.
8 Fushin Ubangiji kuwa ya yi ƙuna a kan Isra’ila har ya sayar da su ga Kushan-Rishatayim sarkin Aram-Naharayim, a wurinsa ne Isra’ilawa suka zama bayi shekara takwas.
And it burned [the] anger of Yahweh on Israel and he sold them in [the] hand of Cushan-Rishathaim [the] king of Aram Naharaim and they served [the] people of Israel Cushan-Rishathaim eight years.
9 Amma da suka yi kuka ga Ubangiji, sai ya tad musu da mai ceto, Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb wanda ya cece su.
And they cried out [the] people of Israel to Yahweh and he raised up Yahweh a deliverer for [the] people of Israel and he delivered them Othniel [the] son of Kenaz [the] brother of Caleb young more than him.
10 Ruhun Ubangiji ya sauko masa, domin yă zama mahukuncin Isra’ila yă kuma je yaƙi. Ubangiji ya bayar da Kushan-Rishatayim sarkin Aram a hannun Otniyel, ya kuwa sha ƙarfinsa.
And it was on him [the] spirit of Yahweh and he judged Israel and he went out to war and he gave Yahweh in hand his Cushan-Rishathaim [the] king of Aram and it prevailed hand his over Cushan-Rishathaim.
11 Saboda haka ƙasar ta zauna da lafiya shekara arba’in har sai da Otniyel ɗan Kenaz ya rasu.
And it was at peace the land forty year[s] and he died Othniel [the] son of Kenaz.
12 Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda sun aikata wannan mugunta sai Ubangiji ya ba wa Eglon sarkin Mowab ƙarfi a kan Isra’ila.
And they repeated [the] people of Israel to do the evil in [the] eyes of Yahweh and he strengthened Yahweh Eglon [the] king of Moab over Israel on for they did the evil in [the] eyes of Yahweh.
13 Da ya sami Ammonawa da Amalekawa suka haɗa hannu tare, sai Eglon ya tafi ya auka wa Isra’ila, suka ƙwace Birnin Dabino.
And he gathered to himself [the] people of Ammon and Amalek and he went and he attacked Israel and they took possession of [the] city of the palm trees.
14 Isra’ilawa suka zama bayin Eglon sarkin Mowab shekara goma sha takwas.
And they served [the] people of Israel Eglon [the] king of Moab eight-teen year[s].
15 Isra’ilawa suka sāke yin kuka ga Ubangiji, ya kuwa ba su mai ceto, Ehud, wani bahago, ɗan Gera daga kabilar Benyamin. Isra’ilawa suka aike shi da haraji wurin Eglon sarkin Mowab.
And they cried out [the] people of Israel to Yahweh and he raised up Yahweh for them a deliverer Ehud [the] son of Gera [the] Ben-jaminite a man impeded [the] hand of right his and they sent [the] people of Israel by hand his tribute to Eglon [the] king of Moab.
16 To, Ehud ya riga ya ƙera takobi mai kaifi biyu mai tsawo wajen kamu ɗaya da rabi, wanda ya yi ɗamara da shi a cinyarsa ta dama ƙarƙashin rigarsa.
And he made for himself Ehud a sword and [belonged] to it two lips [was] a cubit length its and he girded it from under to garments his on [the] thigh of right his.
17 Ya kai wa Eglon sarkin Mowab harajin, wanda yake mai ƙiba ne.
And he brought near the tribute to Eglon [the] king of Moab and Eglon [was] a man fat very.
18 Bayan Ehud ya ba da harajin, sai ya sallame mutanen da suka ɗauko harajin.
And it was just when he had finished to bring near the tribute and he sent away the people [who] bore the tribute.
19 A wajen gumaka kusa da Gilgal, shi kansa ya juya ya koma ya ce, “Ranka yă daɗe, ina da saƙo na asiri dominka.” Sarkin ya ce, “Ku ba mu wuri!” Sai dukan fadawansa suka fita.
And he he returned from the idols which [were] with Gilgal and he said a word of secrecy [belongs] to me to you O king and he said hush! and they went out from with him all those [who] stood with him.
20 Sai Ehud ya matso yayinda shi kuwa yake zaune shi kaɗai a ɗakin sama mai sanyi a fadansa ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah dominka.” Sarki ya tashi daga kujerarsa,
And Ehud - he came to him and he [was] sitting in [the] roof chamber of the coolness which [belonged] to him to only him and he said Ehud a word of God [belongs] to me to you and he rose from on the throne.
21 Ehud ya kai hannun hagunsa, ya zaro takobi daga cinyar ƙafar damansa ya soki sarki a ciki.
And he stretched out Ehud [the] hand of left his and he took the sword from on [the] thigh of right his and he thrust it in belly his.
22 Har ƙotar ma ta shige ciki, takobin kuma ya fito ta bayansa. Ehud bai zare takobin ba, kitse kuwa ya rufe shi.
And it went also the hilt after the blade and it closed up the fat behind the blade that not he drew out the sword from belly his and he went out the hole towards.
23 Sa’an nan Ehud ya fita daga shirayin; ya rufe ƙofar ɗakin saman, ya kuma kulle su.
And he went out Ehud the porch towards and he closed [the] doors of the roof chamber behind him and he locked [them].
24 Bayan da ya tafi, bayin sarki suka zo suka tarar duk ƙofofin ɗakin sama suna kulle, suka ce, “Wataƙila yana bayan gari ne a ɗakin ciki.”
And he he went forth and servants his they came and they saw and there! [the] doors of the roof chamber [were] locked and they said surely [is] covering he feet his in [the] chamber of the coolness.
25 Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ƙofar ba, sai suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe. Sai ga shugabansu a ƙasa matacce.
And they writhed until were ashamed and there! not he [was] opening [the] doors of the roof chamber and they took the key and they opened [them] and there! master their [was] lying [the] ground towards dead.
26 Yayinda suke fama jira, Ehud ya riga ya yi gaba. Ya bi ta wajen gumaka zuwa Seyira.
And Ehud he escaped until delayed they and he he passed by the idols and he escaped Seirah towards.
27 Da ya iso can, sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuma suka gangaro tare da shi daga tuddai, shi kuwa yana jagorarsu.
And it was when came he and he gave a blast on the ram's horn in [the] hill country of Ephraim and they went down with him [the] people of Israel from the hill country and he [was] before them.
28 Ya umarce su ya ce, “Ku bi ni, gama Ubangiji ya ba Mowab abokin gābanku a hannunku.” Haka suka gangaro tare da shi suna mallaki mashigin Urdun da ta shiga zuwa Mowab, ba su yarda wani ya haye ba.
And he said to them pursue after me for he has given Yahweh enemies your Moab in hand your and they went down after him and they captured [the] fords of the Jordan to Moab and not they permitted anyone to pass over.
29 A lokacin sun kashe mutanen Mowab dubu goma, dukansu jarumawa da masu ji da ƙarfi; ba ko ɗaya da ya tsira.
And they struck down Moab at the time that about ten thousand man every stout [person] and every man of strength and not he escaped anyone.
30 A wannan rana aka mai da Mowab bayin Isra’ila, ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya shekara takwas.
And it was subdued Moab on the day that under [the] hand of Israel and it was at peace the land eighty year[s].
31 Bayan Ehud, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya karkashe Filistiyawa ɗari shida da sandar korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra’ila.
And after him he was Shamgar [the] son of Anath and he struck down [the] Philistines six hundred man with [the] goad of cattle and he delivered also he Israel.