< Mahukunta 21 >

1 Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
Torej možje iz Izraela so v Micpi prisegli, rekoč: »Nihče izmed nas svoje hčere ne bo dal Benjaminu za ženo.«
2 Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
Ljudstvo je prišlo k Božji hiši in tam so ostali do večera pred Bogom in povzdignili svoje glasove in bridko jokali
3 Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
in rekli: »Oh Gospod, Izraelov Bog, zakaj se je to zgodilo v Izraelu, da danes manjka en rod v Izraelu.«
4 Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
Pripetilo se je naslednji dan, da je ljudstvo zgodaj vstalo, tam zgradilo oltar in darovalo žgalne daritve in mirovne daritve.
5 Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
Izraelovi otroci so rekli: »Kdo je tam med vsemi Izraelovimi rodovi, ki s skupnostjo ni prišel gor h Gospodu?« Kajti sklenili so veliko prisego glede tistega, ki ne pride gor h Gospodu v Micpo, rekoč: »Ta bo zagotovo usmrčen.«
6 To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
Izraelovim otrokom je bilo žal zaradi Benjamina, njihovega brata in rekli so: »Ta dan je iz Izraela iztrebljen en rod.
7 Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
Kako bomo storili zaradi žena za tiste, ki so ostali, glede na to, da smo pri Gospodu prisegli, da jim ne bomo dali izmed svojih hčera za žene?«
8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
Rekli so: »Kateri izmed Izraelovih rodov je, ki ni prišel v Micpo h Gospodu?« Glej, iz Jabéš Gileáda ni nihče prišel v tabor k zboru.
9 Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
Kajti ljudstvo je bilo prešteto in glej, tam ni bilo nobenega prebivalca iz Jabéš Gileáda.
10 Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
Skupnost je tja poslala dvanajst tisoč mož izmed najhrabrejših in jim zapovedala, rekoč: »Pojdite in udarite prebivalce Jabéš Gileáda z ostrino meča, z ženskami in otroki.
11 Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
To je stvar, ki jo boste storili: ›Popolnoma boste uničili vsakega moškega in vsako žensko, ki je ležala z moškim.‹«
12 Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
Med prebivalci Jabéš Gileáda so našli štiristo mladih devic, ki nobenega moškega niso spoznale z ležanjem s katerimkoli moškim. Privedli so jih v tabor do Šila, ki je v kánaanski deželi.
13 Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
Celotna skupnost je poslala nekatere, da govorijo Benjaminovim otrokom, ki so bili v Rimónovi skali in da miroljubno kličejo k njim.
14 Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
Ob tistem času je ponovno prišel Benjamin in izročili so jim žene, ki so jih žive rešili izmed žensk Jabéš Gileáda in vendar jim to ni zadoščalo.
15 Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
Ljudstvo se je pokesalo zaradi Benjamina, zato ker je Gospod naredil vrzel v Izraelovih rodovih.
16 Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
Potem so starešine skupnosti rekli: »Kako bomo storili glede žena za tiste, ki ostanejo, glede na to, da so ženske uničene iz Benjamina?«
17 Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
Rekli so: » Mora biti dediščina za tiste, ki pobegnejo iz Benjamina, da iz Izraela ne bo uničen rod.«
18 Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
Vendar jim ne moremo dati žene izmed svojih hčera, kajti Izraelovi otroci so prisegli, rekoč: »Preklet bodi, kdor daje ženo Benjaminu.«
19 Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
Potem so rekli: »Glej, tam je letno Gospodovo praznovanje v Šilu, na kraju, ki je na severni strani Betela, na vzhodni strani glavne ceste, ki gre gor od Betela do Sihema in na vzhodni strani Lebóne.«
20 Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
Zato so Benjaminovim otrokom zapovedali, rekoč: »Pojdite in prežite v zasedi v vinogradih.
21 ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
Glejte in opazujte, če hčere iz Šila pridejo ven, da plešejo v plesih, potem pridite iz vinogradov in zgrabite vsak mož svojo ženo izmed hčera v Šilu in pojdite v Benjaminovo deželo.«
22 Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
Zgodilo se bo, da ko pridejo k nam njihovi očetje ali njihovi bratje, da se pritožujejo, jim bomo rekli: »Bodite jim naklonjeni zaradi nas, ker v vojni nismo prihranili vsakemu možu svoje žene, kajti ob tistem času jim jih vi niste dali, tako ste sedaj krivi.«
23 Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
Benjaminovi otroci so tako storili in si vzeli žene, glede na njihovo število izmed tistih, ki so plesale, ki so jih ujeli in odšli ter se vrnili v svojo dediščino in popravili mesta in prebivali v njih.
24 A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
Ob tem času so Izraelovi otroci odšli od tam, vsak mož k svojemu rodu in k svoji družini in odšli so od tam, vsak mož k svoji dediščini.
25 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.
V tistih dneh ni bilo kralja v Izraelu. Vsak mož je počel to, kar je bilo pravilno v njegovih lastnih očeh.

< Mahukunta 21 >