< Mahukunta 21 >

1 Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
I Mispa hadde Israels menn svoret: Ingen av oss skal gi nogen i Benjamin sin datter til hustru.
2 Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
Men da folket kom til Betel, satt de der for Guds åsyn til om aftenen, og de gråt høit og lenge
3 Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
og sa: Herre, Israels Gud, hvorfor har dette hendt i Israel at det i dag fattes en hel stamme av Israel?
4 Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
Den følgende dag stod folket tidlig op og bygget et alter der og ofret brennoffer og takkoffer.
5 Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
Og Israels barn sa: Hvem var det blandt alle Israels stammer som ikke kom op til Herren med menigheten? For de hadde svoret en dyr ed at den som ikke kom op til Herren i Mispa, han skulde late livet.
6 To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
Det gjorde Israels barn ondt for Benjamin, deres bror, og de sa: Idag er det hugget bort en stamme av Israel.
7 Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
Hvad skal vi gjøre for dem som er tilbake, så de kan få sig hustruer, siden vi har svoret ved Herren at vi ikke vil gi dem nogen av våre døtre til ekte?
8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
Så sa de: Var det nogen blandt Israels ætter som ikke kom op til Herren i Mispa? Da fikk de vite at fra Jabes i Gilead var ingen kommet til leiren, til møtet.
9 Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
For da folket blev mønstret, viste det sig at ingen av innbyggerne i Jabes i Gilead var der.
10 Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
Da sendte menigheten tolv tusen mann av krigsfolket dit og bød dem: Dra avsted og slå innbyggerne i Jabes i Gilead med sverdets egg, også kvinner og barn!
11 Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
Således skal I gjøre: Alt mannkjønn og hver kvinne som har hatt samleie med nogen mann, skal I slå med bann.
12 Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
Da fant de blandt innbyggerne i Jabes i Gilead fire hundre jomfruer som ikke hadde vært nær nogen mann og hatt samleie med ham; dem tok de med sig til leiren i Silo i Kana'ans land.
13 Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
Og hele menigheten sendte bud til Benjamins barn, som var på Rimmons klippe, og lovte dem fred.
14 Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
Da vendte Benjamin med én gang tilbake, og de gav dem de kvinner som de hadde latt bli i live blandt kvinnene i Jabes i Gilead; men det blev ikke nok for dem.
15 Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
Og det gjorde folket ondt for Benjamin; for Herren hadde gjort et skår i Israels stammer.
16 Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
Og menighetens eldste sa: Hvad skal vi gjøre for dem som ennu er tilbake, så de kan få sig hustruer, siden alle kvinner i Benjamin er utryddet?
17 Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
Og de sa: Benjamins arvedel skal høre de undkomne til, så ikke en hel stamme i Israel skal utslettes.
18 Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
Men vi kan ikke gi dem nogen av våre døtre til ekte. For Israels barn har svoret: Forbannet være den som gir nogen av Benjamin sin datter til hustru!
19 Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
Så sa de: År for år holdes det jo en høitid for Herren i Silo, som ligger nordenfor Betel, østenfor alfarveien som fører fra Betel op til Sikem, og sønnenfor Lebona.
20 Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
Og de sa til Benjamins barn: Gå og legg eder på lur i vingårdene
21 ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
og pass på, og når I ser Silos døtre gå ut til dans, da skal I springe frem fra vingårdene og røve eder hver sin hustru blandt Silos døtre og så dra hjem til Benjamins land.
22 Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
Og når deres fedre eller brødre kommer og vil gå i rette med oss, da skal vi si til dem: Unn oss dem! For vi har ikke alle fått oss hustruer i krigen, og I har jo ikke selv gitt dem pikene; da vilde I nu være skyldige.
23 Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
Og Benjamins barn gjorde således og tok sig hver sin hustru, så mange som de var, blandt de dansende kvinner som de røvet; og de drog avsted og vendte tilbake til sin arvedel og bygget op igjen byene og blev boende der.
24 A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
På samme tid reiste Israels barn også derfra, hver til sin stamme og sin ætt; de drog bort derfra, hver til sin arvedel.
25 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.
I de dager var det ingen konge i Israel; hver mann gjorde hvad rett var i hans øine.

< Mahukunta 21 >