< Mahukunta 21 >
1 Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
Or, les Israélites avaient juré, à Miçpa, que nul d’entre eux ne donnerait sa fille pour épouse à un Benjamite.
2 Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
Le peuple vainqueur se rendit à Béthel, y resta jusqu’au soir en présence du Seigneur, élevant la voix et versant d’abondantes larmes.
3 Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
Ils disaient: "Eternel, Dieu d’Israël! pourquoi faut-il qu’Israël ait ce malheur de se voir privé d’une tribu entière?"
4 Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
Dès le lendemain de bonne heure, le peuple bâtit là un autel, offrit des holocaustes et des rémunératoires.
5 Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
Puis ils se demandèrent qui d’entre les tribus d’Israël n’était pas venu à l’assemblée tenue devant l’Eternel; car un serment solennel avait menacé de mort quiconque ne serait pas venu à Miçpa devant l’Eternel.
6 To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
Et maintenant les enfants d’Israël s’affligeaient au sujet de Benjamin leur frère, et ils disaient: "Une tribu a été retranchée aujourd’hui d’Israël l
7 Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
Que ferons-nous pour procurer des femmes à ceux qui restent, alors que nous avons juré par l’Eternel de ne pas leur permettre d’épouser nos filles?
8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
C’Est alors qu’ils s’informèrent si quelqu’un, parmi les tribus d’Israël, ne s’était pas rendu à Miçpa devant l’Eternel, et il se trouva que nul homme de Jabès-Galaad n’était venu au camp, dans la réunion.
9 Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
En effet, le peuple avait été dénombré, et aucun des habitants de Jabès-Galaad n’y figurait.
10 Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
L’Assemblée y envoya donc douze mille guerriers, en leur donnant cet ordre: "Allez à Jabès-Galaad, et passez les habitants au fil de l’épée, même les femmes et les enfants,
11 Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
en observant toutefois cette règle, de vouer à la mort tous les mâles et toutes les femmes ayant déjà cohabité avec un homme."
12 Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
Or, sur les habitants de Jabès-Galaad, il se trouva quatre cents jeunes filles, encore vierges, n’ayant eu aucun contact avec un homme; et on les conduisit au camp à Silo, qui est dans le pays de Canaan.
13 Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
Alors toute l’assemblée envoya un message aux Benjamites réfugiés à la Roche de Rimmon et leur offrit la paix.
14 Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
Les Benjamites revinrent aussitôt, et on leur donna les femmes qu’on avait épargnées parmi celles de Jabès-Galaad; mais il ne s’en trouva pas autant qu’il fallait.
15 Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
Or, le peuple était ému au sujet de Benjamin, en songeant à la brèche que le Seigneur avait faite parmi les tribus d’Israël.
16 Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
Les anciens de la communauté dirent: "Comment pourvoirons-nous de femmes ceux qui restent encore, toute femme en Benjamin ayant été exterminée?"
17 Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
Ils ajoutaient: "Ceux qui ont échappé auront l’héritage de Benjamin; il ne faut pas qu’une tribu disparaisse en Israël!
18 Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
Pour nous, nous ne pouvons leur donner nos filles pour femmes, puisque les enfants d’Israël ont prononcé ce serment: "Maudit qui donnerait une femme à Benjamin!"
19 Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
Mais il y a, dirent-ils, une fête religieuse célébrée chaque année à Silo, sur la place qui est au nord de Béthel, à l’orient de la route qui monte de Béthel à Sichem, et au midi de Lebona."
20 Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
Ils donnèrent donc ce conseil aux Benjamites: Allez vous embusquer dans les vignes;
21 ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
et lorsque vous verrez les filles de Silo sortir pour danser en chœur, vous sortirez vous-mêmes des vignes, vous enlèverez chacun une femme parmi les filles de Silo, et vous vous en irez au pays de Benjamin.
22 Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
Que si leurs pères ou leurs frères viennent se plaindre à nous, nous leur dirons: Faites-leur grâce en notre faveur, puisque nous n’avons pu prendre une femme pour chacun lors de l’expédition; d’ailleurs, ce n’est pas vous qui les leur avez données, pour vous croire à cette heure en faute."
23 Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
Ainsi firent les enfants de Benjamin: ils enlevèrent, parmi les danseuses, un nombre de femmes égal au leur et les prirent pour épouses; puis ils s’en retournèrent dans leur territoire héréditaire, rebâtirent les villes et s’y établirent.
24 A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
Les enfants d’Israël s’en allèrent alors, chacun selon sa tribu et sa famille, et chacun s’achemina de là à son héritage.
25 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.
En ce temps-là il n’y avait point de roi en Israël, et chacun faisait ce que bon lui semblait.