< Mahukunta 21 >
1 Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
Les hommes d'Israël avaient juré à Mitspa, en disant: « Aucun de nous ne donnera sa fille pour femme à Benjamin. »
2 Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
Le peuple vint à Béthel et s'assit jusqu'au soir devant Dieu; il éleva la voix et pleura abondamment.
3 Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
Ils dirent: « Yahvé, le Dieu d'Israël, pourquoi cela est-il arrivé en Israël, qu'il manque aujourd'hui une tribu en Israël? »
4 Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
Le lendemain, le peuple se leva de bonne heure, construisit un autel à cet endroit, et offrit des holocaustes et des sacrifices de prospérité.
5 Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
Les enfants d'Israël dirent: « Qui est, parmi toutes les tribus d'Israël, celui qui n'est pas monté à l'assemblée vers l'Éternel? » Car ils avaient fait un grand serment au sujet de celui qui n'était pas monté vers l'Éternel à Mitspa, en disant: « Il sera certainement mis à mort. »
6 To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
Les enfants d'Israël s'affligèrent pour Benjamin, leur frère, et dirent: « Il y a aujourd'hui une tribu retranchée d'Israël.
7 Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
Comment fournirons-nous des femmes à ceux qui restent, puisque nous avons juré par l'Éternel de ne pas leur donner de nos filles pour femmes? »
8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
Ils dirent: « Quel est celui des tribus d'Israël qui n'est pas monté vers l'Éternel à Mitspa? » Voici, personne n'est venu de Jabesh Galaad au camp, pour l'assemblée.
9 Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
Car lorsqu'on fit le compte du peuple, voici, il n'y avait là aucun des habitants de Jabesh Galaad.
10 Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
L'assemblée y envoya douze mille hommes parmi les plus vaillants, et leur donna cet ordre: « Allez frapper du tranchant de l'épée les habitants de Jabesh Galaad, les femmes et les petits enfants.
11 Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
Voici ce que vous ferez: vous détruirez par interdit tout mâle et toute femme qui a couché avec un homme. »
12 Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
Ils trouvèrent parmi les habitants de Jabesh Galaad quatre cents jeunes vierges qui n'avaient pas connu l'homme en couchant avec lui, et ils les amenèrent au camp à Silo, qui est au pays de Canaan.
13 Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
Toute l'assemblée envoya parler aux fils de Benjamin qui étaient au rocher de Rimmon, et leur annonça la paix.
14 Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
Benjamin revint à ce moment-là, et ils leur donnèrent les femmes qu'ils avaient sauvées vivantes parmi les femmes de Jabesh Galaad. Il n'y en avait toujours pas assez pour eux.
15 Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
Le peuple s'affligea pour Benjamin, car Yahvé avait fait une brèche dans les tribus d'Israël.
16 Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
Les anciens de l'assemblée dirent: « Comment pourrions-nous fournir des femmes à ceux qui restent, puisque les femmes sont détruites hors de Benjamin? »
17 Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
Ils dirent: « Il faut qu'il y ait un héritage pour ceux qui sont échappés de Benjamin, afin qu'une tribu ne soit pas effacée d'Israël.
18 Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
Mais nous ne pouvons pas leur donner des femmes de nos filles, car les enfants d'Israël ont juré en disant: « Maudit soit celui qui donne une femme à Benjamin. »
19 Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
Ils dirent: « Voici qu'il y a une fête de l'Éternel d'année en année à Silo, qui est au nord de Béthel, à l'est de la route qui monte de Béthel à Sichem, et au sud de Lebona. »
20 Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
Ils donnèrent cet ordre aux fils de Benjamin: « Allez vous poster dans les vignes,
21 ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
et regardez, et voici, si les filles de Silo sortent pour danser dans les bals, sortez des vignes, prenez chacun sa femme parmi les filles de Silo, et allez au pays de Benjamin.
22 Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
Lorsque leurs pères ou leurs frères viendront se plaindre à nous, nous leur dirons: « Accordez-nous leur grâce, car nous n'avons pas pris pour chacun sa femme dans la bataille, et vous ne les leur avez pas données, sinon vous seriez maintenant coupables. »
23 Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
Les fils de Benjamin firent de même et prirent des femmes selon leur nombre, de celles qui dansaient et qu'ils enlevèrent. Ils partirent et retournèrent dans leur héritage, bâtirent les villes et y habitèrent.
24 A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
En ce temps-là, les enfants d'Israël partirent de là, chacun dans sa tribu et dans sa famille, et ils s'en allèrent chacun dans son héritage.
25 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.
En ce temps-là, il n'y avait pas de roi en Israël. Chacun faisait ce qui était juste à ses propres yeux.