< Mahukunta 21 >
1 Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
And [the] man of Israel he had sworn at Mizpah saying anyone of us not he will give daughter his to Benjamin to a wife.
2 Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
And it came the people Beth-el and they sat there until the evening before God and they lifted up voice their and they wept weeping great.
3 Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
And they said why? O Yahweh [the] God of Israel has it happened (this [thing] *LA(bh)*) in Israel to be missing this day from Israel a tribe one.
4 Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
And it was from [the] next day and they rose early the people and they built there an altar and they offered up burnt offerings and peace offerings.
5 Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
And they said [the] people of Israel who? [is [the] one] who not he went up in the assembly from all [the] tribes of Israel to Yahweh for the oath great it was to [the one] who not he went up to Yahweh Mizpah saying certainly he will be put to death.
6 To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
And they had compassion [the] people of Israel to Benjamin brother its and they said it has been cut off this day a tribe one from Israel.
7 Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
What? will we do for them for [those who] remain for wives and we we have sworn by Yahweh to not to give to them any of daughters our to wives.
8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
And they said who? [is the] one from [the] tribes of Israel which not it went up to Yahweh Mizpah and there! not he had come anyone to the camp from Jabesh Gilead to the assembly.
9 Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
And it was mustered the people and there! there not there [was] anyone from [the] inhabitants of Jabesh Gilead.
10 Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
And they sent there the congregation two [plus] ten thousand man from [the] sons of strength and they commanded them saying go and you will strike [the] inhabitants of Jabesh Gilead to [the] mouth of [the] sword and the women and the little one[s].
11 Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
And this [is] the thing which you will do every male and every woman [who] has known lying of a male you will totally destroy.
12 Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
And they found of [the] inhabitants of - Jabesh Gilead four hundred young woman virgin[s] who not she had known a man to lying of a male and they brought them to the camp Shiloh which [is] in [the] land of Canaan.
13 Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
And they sent all the congregation and they spoke to [the] descendants of Benjamin who [were] at [the] rock of Rimmon and they proclaimed to them peace.
14 Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
And it returned Benjamin at the time that and they gave to them the women whom they had preserved alive from [the] women of Jabesh Gilead and not they found for them so.
15 Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
And the people it had compassion to Benjamin for he had made Yahweh a breach in [the] tribes of Israel.
16 Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
And they said [the] elders of the congregation what? will we do for [those who] remain for wives for she is destroyed from Benjamin woman.
17 Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
And they said a possession of [the] escaped remnant [belongs] to Benjamin and not it will be wiped out a tribe from Israel.
18 Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
And we not we are able to give to them wives any of daughters our for they had sworn [the] people of Israel saying [be] cursed [one who] gives a wife to Benjamin.
19 Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
And they said here! [the] festival of Yahweh [is] in Shiloh from days - days towards which [is] from north-ward of Beth-el [the] rising of towards the sun of [the] highway which goes up from Beth-el Shechem towards and from [the] south to Lebonah.
20 Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
(And they commanded *Q(K)*) [the] descendants of Benjamin saying go and you will lie in wait in the vineyards.
21 ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
And you will see and there! if they will come out [the] daughters of Shiloh to dance in dances and you will go out from the vineyards and you will seize for yourselves each man wife his from [the] daughters of Shiloh and you will go [the] land of Benjamin.
22 Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
And it will be that they will come fathers their or brothers their (to make a complaint *Q(k)*) to us and we will say to them show favor for to us them for not we took each man wife his in the battle for not you you gave [them] to them about this time you will be guilty.
23 Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
And they did thus [the] descendants of Benjamin and they carried off wives to number their from the dancers whom they seized and they went and they returned to inheritance their and they rebuilt the cities and they dwelt in them.
24 A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
And they dispersed from there [the] people of Israel at the time that each man to tribe his and to clan his and they went out from there each man to inheritance his.
25 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.
In the days those there not [was] a king in Israel each man the right in own eyes his he will do.