< Mahukunta 21 >

1 Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
Now the men of Israel had sworn in Mizpah, saying, "There shall not any of us give his daughter to Benjamin as wife."
2 Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
The people came to Bethel, and sat there until evening before God, and lifted up their voices, and wept severely.
3 Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
They said, "LORD God of Israel, why has this happened in Israel, that there should be today one tribe lacking in Israel?"
4 Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
It happened on the next day that the people rose early, and built there an altar, and offered burnt offerings and peace offerings.
5 Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
The children of Israel said, "Who is there among all the tribes of Israel who did not come up in the assembly to the LORD?" For they had made a great oath concerning anyone who did not come up to the LORD to Mizpah, saying, "He shall surely be put to death."
6 To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
The children of Israel grieved for Benjamin their brother, and said, "There is one tribe cut off from Israel this day.
7 Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
How shall we do for wives for those who remain, seeing we have sworn by the LORD that we will not give them of our daughters to wives?"
8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
They said, "What one is there of the tribes of Israel who did not come up to the LORD to Mizpah?" Look, no one came to the camp from Jabesh Gilead to the assembly.
9 Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
For when the people were numbered, look, there were none of the inhabitants of Jabesh Gilead there.
10 Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
The congregation sent there twelve thousand men of the most valiant, and commanded them, saying, "Go and strike the inhabitants of Jabesh Gilead with the edge of the sword, with the women and the little ones.
11 Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
This is the thing that you shall do: you shall utterly destroy every male, and every woman who has slept with a man, but the virgins you are to keep alive." And they did so.
12 Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
They found among the inhabitants of Jabesh Gilead four hundred young virgins who had never slept with a man; and they brought them to the camp to Shiloh, which is in the land of Canaan.
13 Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
The whole congregation sent and spoke to the people of Benjamin who were in the rock of Rimmon, and proclaimed peace to them.
14 Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
Benjamin returned at that time; and they gave them the women whom they had saved alive of the women of Jabesh Gilead: and yet so they weren't enough for them.
15 Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
The people grieved for Benjamin, because the LORD had made a gap in the tribes of Israel.
16 Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
Then the elders of the congregation said, "How shall we provide wives for those who remain, since the women of Benjamin have been destroyed?"
17 Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
They said, "How will an inheritance remain for the survivors of Benjamin, that a tribe not be blotted out from Israel.
18 Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
However we may not give them wives of our daughters, for the children of Israel had sworn, saying, 'Cursed is he who gives a wife to Benjamin.'"
19 Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
They said, "Look, there is a feast of the LORD from year to year in Shiloh, which is on the north of Bethel, on the east side of the highway that goes up from Bethel to Shechem, and on the south of Lebonah."
20 Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
They commanded the people of Benjamin, saying, "Go and lie in wait in the vineyards,
21 ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
and watch. If the daughters of Shiloh come out to dance in the dances, then come out of the vineyards, and each man catch his wife from the daughters of Shiloh, and go to the land of Benjamin.
22 Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
It shall be, when their fathers or their brothers come to complain to us, that we will say to them, 'Grant them graciously to us, because we didn't take wives for each man in battle, neither did you give them to them, otherwise you would now be guilty.'"
23 Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
The people of Benjamin did so, and took them wives, according to their number, of those who danced, whom they carried off. They went and returned to their inheritance, built the cities, and lived in them.
24 A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
The children of Israel departed there at that time, every man to his tribe and to his family, and they went out from there every man to his inheritance.
25 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.
In those days there was no king in Israel: every man did that which was right in his own eyes.

< Mahukunta 21 >