< Mahukunta 20 >

1 Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
و جمیع بنی‌اسرائیل بیرون آمدند وجماعت مثل شخص واحد از دان تابئرشبع با اهل زمین جلعاد نزد خداوند در مصفه جمع شدند.۱
2 Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
و سروران تمام قوم و جمیع اسباطاسرائیل یعنی چهارصد هزار مرد شمشیر زن پیاده در جماعت قوم خدا حاضر بودند.۲
3 (Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
وبنی بنیامین شنیدند که بنی‌اسرائیل در مصفه برآمده‌اند. و بنی‌اسرائیل گفتند: «بگویید که این عمل زشت چگونه شده است.»۳
4 Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
آن مرد لاوی که شوهر زن مقتوله بود، در جواب گفت: «من با کنیزخود به جبعه که از آن بنیامین باشد، آمدیم تا شب را بسر بریم.۴
5 Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
و اهل جبعه بر من برخاسته، خانه رادر شب، گرد من احاطه کردند، و مرا خواستندبکشند و کنیز مرا ذلیل نمودند که بمرد.۵
6 Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
و کنیز خود را گرفته، او را قطعه قطعه کردم و او را درتمامی ولایت ملک اسرائیل فرستادم، زیرا که کارقبیح و زشت در اسرائیل نمودند.۶
7 To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
هان جمیع شما، ای بنی‌اسرائیل حکم و مشورت خود رااینجا بیاورید.»۷
8 Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
آنگاه تمام قوم مثل شخص واحد برخاسته، گفتند: «هیچ کدام از ما به خیمه خود نخواهیم رفت، و هیچ کدام از ما به خانه خود بر نخواهیم گشت.۸
9 Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
و حال کاری که به جبعه خواهیم کرد این است که به حسب قرعه بر آن برآییم.۹
10 Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
و ده نفراز صد و صد از هزار و هزار از ده هزار از تمامی اسباط اسرائیل بگیریم تا آذوقه برای قوم بیاورند، و تا چون به جبعه بنیامینی برسند با ایشان موافق همه قباحتی که در اسرائیل نموده‌اند، رفتارنمایند.»۱۰
11 Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
پس جمیع مردان اسرائیل بر شهر جمع شده، مثل شخص واحد متحد شدند.۱۱
12 Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
و اسباطاسرائیل اشخاصی چند در تمامی سبط بنیامین فرستاده، گفتند: «این چه شرارتی است که در میان شما واقع شده است؟۱۲
13 Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
پس الان آن مردان بنی بلیعال را که در جبعه هستند، تسلیم نمایید تاآنها را به قتل رسانیم، و بدی را از اسرائیل دورکنیم.» اما بنیامینیان نخواستند که سخن برادران خود بنی‌اسرائیل را بشنوند.۱۳
14 Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
و بنی بنیامین ازشهرهای خود به جبعه جمع شدند تا بیرون رفته، با بنی‌اسرائیل جنگ نمایند.۱۴
15 Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
و از بنی بنیامین درآن روز بیست و ششهزار مرد شمشیرزن ازشهرها سان دیده شد، غیر از ساکنان جبعه که هفتصد نفر برگزیده، سان دیده شد.۱۵
16 Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
و از تمام این گروه هفتصد نفر چپ دست برگزیده شدند که هر یکی از آنها مویی را به سنگ فلاخن می‌زدند وخطا نمی کردند.۱۶
17 Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
و از مردان اسرائیل سوای بنیامینیان چهارصد هزار مرد شمشیرزن سان دیده شد که جمیع اینها مردان جنگی بودند.۱۷
18 Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
و بنی‌اسرائیل برخاسته، به بیت ئیل رفتند واز خدا مشورت خواسته، گفتند: «کیست که اولااز ما برای جنگ نمودن با بنی بنیامین برآید؟» خداوند گفت: «یهودا اول برآید.»۱۸
19 Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
و بنی‌اسرائیل بامدادان برخاسته، در برابرجبعه اردو زدند.۱۹
20 Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
و مردان اسرائیل بیرون رفتندتا با بنیامینیان جنگ نمایند، و مردان اسرائیل برابر ایشان در جبعه صف آرایی کردند.۲۰
21 Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
وبنی بنیامین از جبعه بیرون آمده، در آن روز بیست و دو هزار نفر از اسرائیل را بر زمین هلاک کردند.۲۱
22 Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
و قوم، یعنی مردان اسرائیل خود را قوی‌دل ساخته، بار دیگر صف آرایی نمودند، در مکانی که روز اول صف آرایی کرده بودند.۲۲
23 Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
وبنی‌اسرائیل برآمده، به حضور خداوند تا شام گریه کردند، و از خداوند مشورت خواسته، گفتند: «آیا بار دیگر نزدیک بشوم تا با برادران خود بنی بنیامین جنگ نمایم؟» خداوند گفت: «به مقابله ایشان برآیید.»۲۳
24 Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
و بنی‌اسرائیل در روز دوم به مقابله بنی بنیامین پیش آمدند.۲۴
25 A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
و بنیامینیان در روزدوم به مقابله ایشان از جبعه بیرون شده، بار دیگرهجده هزار نفر از بنی‌اسرائیل را بر زمین هلاک ساختند که جمیع اینها شمشیرزن بودند.۲۵
26 Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
آنگاه تمامی بنی‌اسرائیل، یعنی تمامی قوم برآمده، به بیت ئیل رفتند و گریه کرده، در آنجا به حضور خداوند توقف نمودند، و آن روز را تا شام روزه داشته، قربانی های سوختنی و ذبایح سلامتی به حضور خداوند گذرانیدند.۲۶
27 Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
و بنی‌اسرائیل از خداوند مشورت خواستند. وتابوت عهد خدا آن روزها در آنجا بود.۲۷
28 Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
وفینحاس بن العازار بن هارون در آن روزها پیش آن ایستاده بود، و گفتند: «آیا بار دیگر بیرون روم و بابرادران خود بنی بنیامین جنگ کنم یا دست بردارم؟» خداوند گفت: «برآی زیرا که فردا او رابه‌دست تو تسلیم خواهم نمود.»۲۸
29 Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
پس اسرائیل در هر طرف جبعه کمین ساختند.۲۹
30 Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
و بنی‌اسرائیل در روز سوم به مقابله بنی بنیامین برآمدند، و مثل سابق در برابر جبعه صف آرایی نمودند.۳۰
31 Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
و بنی بنیامین به مقابله قوم بیرون آمده، از شهر کشیده شدند و به زدن و کشتن قوم در راهها که یکی از آنها به سوی بیت ئیل ودیگری به سوی جبعه می‌رود مثل سابق شروع کردند، و به قدر سی نفر از اسرائیل در صحراکشته شدند.۳۱
32 Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
و بنی بنیامین گفتند که «ایشان مثل سابق پیش ما منهزم شدند.» اما بنی‌اسرائیل گفتند: «بگریزیم تا ایشان را از شهر به راههابکشیم.»۳۲
33 Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
و تمامی مردان اسرائیل از مکان خودبرخاسته، در بعل تامار صف آرایی نمودند، وکمین کنندگان اسرائیل از مکان خود یعنی از معره جبعه به در جستند.۳۳
34 Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
و ده هزار مرد برگزیده ازتمام اسرائیل در برابر جبعه آمدند و جنگ سخت شد، و ایشان نمی دانستند که بلا بر ایشان رسیده است.۳۴
35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
و خداوند بنیامین را به حضور اسرائیل مغلوب ساخت و بنی‌اسرائیل در آن روز بیست وپنجهزار و یکصد نفر را از بنیامین هلاک ساختندکه جمیع ایشان شمشیرزن بودند.۳۵
36 Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
و بنی بنیامین دیدند که شکست یافته اندزیرا که مردان اسرائیل به بنیامینیان جا داده بودند، چونکه اعتماد داشتند بر کمینی که به اطراف جبعه نشانده بودند.۳۶
37 Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
و کمین کنندگان تعجیل نموده، بر جبعه هجوم آوردند و کمین کنندگان خود را پراکنده ساخته، تمام شهر را به دم شمشیرزدند.۳۷
38 Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
و در میان مردان اسرائیل و کمین کنندگان علامتی قرار داده شد که تراکم دود بسیار بلند ازشهر برافرازند.۳۸
39 a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
پس چون مردان اسرائیل درجنگ رو گردانیدند، بنیامینیان شروع کردند به زدن و کشتن قریب سی نفر از مردان اسرائیل زیراگفتند یقین ایشان مثل جنگ اول از حضور ماشکست یافته‌اند.۳۹
40 Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
و چون آن تراکم ستون دوداز شهر بلند شدن گرفت، بنیامینیان از عقب خودنگریستند و اینک تمام شهر به سوی آسمان به دود بالا می‌رود.۴۰
41 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
و بنی‌اسرائیل برگشتند وبنیامینیان پریشان شدند، زیرا دیدند که بلا برایشان رسیده است.۴۱
42 Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
پس از حضور مردان اسرائیل به راه صحرا روگردانیدند. اما جنگ، ایشان را در‌گرفت و آنانی که از شهر بیرون آمدندایشان را در میان، هلاک ساختند.۴۲
43 Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
پس بنیامینیان را احاطه کرده، ایشان را تعاقب نمودند، و در منوحه در مقابل جبعه به سوی طلوع آفتاب ایشان را پایمال کردند.۴۳
44 Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
و هجده هزار نفر ازبنیامین که جمیع ایشان مردان جنگی بودند، افتادند.۴۴
45 Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
و ایشان برگشته، به سوی صحرا تاصخره رمون بگریختند. و پنج هزار نفر از ایشان را به‌سر راهها هلاک کردند، و ایشان را تا جدعوم تعاقب کرده، دو هزار نفر از ایشان را کشتند.۴۵
46 A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
پس جمیع کسانی که در آن روز از بنیامین افتادند، بیست و پنج هزار مرد شمشیرزن بودندکه جمیع آنها مردان جنگی بودند.۴۶
47 Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
اما ششصدنفر برگشته، به سوی بیابان به صخره رمون فرارکردند، و در صخره رمون چهار ماه بماندند.۴۷
48 Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.
ومردان اسرائیل بر بنیامینیان برگشته، ایشان را به دم شمشیر کشتند، یعنی تمام اهل شهر و بهایم وهرچه را که یافتند و همچنین همه شهرهایی را که به آنها رسیدند، به آتش سوزانیدند.۴۸

< Mahukunta 20 >