< Mahukunta 20 >
1 Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
Tous les enfants d’Israël sortirent, depuis Dan jusqu’à Bersabée et au pays de Galaad, et l’assemblée se réunit comme un seul homme devant Yahweh à Maspha.
2 Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
Les chefs de tout le peuple, toutes les tribus d’Israël, se présentèrent dans l’assemblée du peuple de Dieu: quatre cent mille hommes de pied tirant l’épée.
3 (Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
Et les fils de Benjamin apprirent que les enfants d’Israël étaient montés à Maspha. Les enfants d’Israël dirent: « Parlez: comment ce crime a-t-il été commis! »
4 Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
Alors le Lévite, le mari de la femme qui avait été tuée, prit la parole et dit: « J’étais entré à Gabaa de Benjamin, moi et ma concubine, pour y passer la nuit.
5 Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
Les habitants de Gabaa se sont levés contre moi et ont entouré pendant la nuit la maison où j’étais; ils avaient l’intention de me tuer, et ils ont fait violence à ma concubine, et elle est morte.
6 Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
J’ai saisi ma concubine, je l’ai coupée en morceaux, et je l’ai envoyée dans tout le territoire de l’héritage d’Israël; car ils ont commis un crime et une infamie en Israël.
7 To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
Vous voici tous, enfants d’Israël; consultez-vous, et décidez ici même. »
8 Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
Tout le peuple se leva comme un seul homme en disant: « Nul d’entre nous n’ira dans sa tente, nul ne retournera dans sa maison.
9 Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
Voici maintenant ce que nous ferons à Gabaa: Contre elle d’après le sort!
10 Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
Nous prendrons dans toutes les tribus d’Israël dix hommes sur cent, cent sur mille, et mille sur dix mille; ils iront chercher des vivres pour le peuple, afin qu’à leur arrivée on traite Gabaa de Benjamin selon toute l’infamie qu’elle a commise en Israël. »
11 Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
C’est ainsi que tous les hommes d’Israël s’assemblèrent contre la ville, unis comme un seul homme.
12 Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
Les tribus d’Israël envoyèrent des hommes dans toutes les familles de Benjamin pour dire: « Qu’est-ce que ce crime qui a été commis chez vous?
13 Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
Livrez maintenant les hommes pervers qui sont à Gabaa, afin que nous les fassions mourir et que nous ôtions le mal du milieu d’Israël. » Mais les Benjamites ne voulurent pas écouter la voix de leurs frères les enfants d’Israël.
14 Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
Les fils de Benjamin, sortant de leurs villes, s’assemblèrent à Gabaa pour partir en guerre contre les enfants d’Israël.
15 Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
Les fils de Benjamin, sortis des villes, furent recensés en ce jour au nombre de vingt-six mille, tirant l’épée, sans compter les habitants de Gabaa, formant sept cents hommes d’élite.
16 Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
Parmi tout ce peuple il y avait sept cents hommes d’élite qui ne se servaient pas de la main droite; tous ces combattants pouvaient lancer avec la fronde une pierre à un cheveu, sans le manquer.
17 Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
Le nombre des hommes d’Israël recensés, non compris ceux de Benjamin, fut de quatre cent mille tirant l’épée, tous gens de guerre.
18 Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
Et les enfants d’Israël, s’étant levés, montèrent à Béthel, et consultèrent Dieu, en disant: « Qui de nous montera le premier pour combattre les fils de Benjamin? » Yahweh répondit: « Que Juda monte le premier. »
19 Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
Les enfants d’Israël se mirent en marche dès le matin, et ils campèrent contre Gabaa.
20 Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
Les hommes d’Israël s’avancèrent pour combattre ceux de Benjamin, et les hommes d’Israël se rangèrent en bataille contre eux, devant Gabaa.
21 Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
Alors les fils de Benjamin sortirent de Gabaa, et ils couchèrent par terre ce jour-là vingt-deux mille hommes d’Israël.
22 Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
Le peuple, savoir les hommes d’Israël, affermirent leur courage, et ils se rangèrent de nouveau en bataille dans le lieu où ils s’étaient placés le premier jour.
23 Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
Et les enfants d’Israël montèrent et ils pleurèrent devant Yahweh jusqu’au soir; et ils consultèrent Yahweh, en disant: « Marcherai-je encore pour combattre les fils de Benjamin, mon frère? » Yahweh répondit: « Montez contre lui. »
24 Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
Les enfants d’Israël s’approchèrent des fils de Benjamin, le second jour;
25 A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
et, ce second jour, les fils de Benjamin sortirent de Gabaa à leur rencontre, et ils couchèrent encore par terre dix-huit mille hommes des enfants d’Israël, tous tirant l’épée.
26 Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
Tous les enfants d’Israël et tout le peuple montèrent et vinrent à Béthel; ils pleurèrent, assis là devant Yahweh; ils jeûnèrent en ce jour jusqu’au soir, et ils offrirent des holocaustes et des sacrifices pacifiques devant Yahweh.
27 Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
Et les enfants d’Israël consultèrent Yahweh, — en ces jours-là, l’arche de l’alliance de Dieu était là,
28 Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
et Phinées, fils d’Eléazar, fils d’Aaron, se tenait devant elle, en ces jours, — et ils dirent: « Marcherai-je encore pour combattre les fils de Benjamin, mon frère, ou bien dois-je cesser? » Yahweh répondit: « Montez, car demain je les livrerai en ta main. »
29 Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
Alors Israël plaça une embuscade autour de Gabaa,
30 Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
et, le troisième jour, les enfants d’Israël montèrent contre les fils de Benjamin; ils se rangèrent en bataille devant Gabaa, comme les autres fois.
31 Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
Et les fils de Benjamin sortirent à la rencontre du peuple, en se laissant attirer loin de la ville. Ils commencèrent à frapper et à tuer parmi le peuple, comme les autres fois, sur les routes dont l’une monte à Béthel et l’autre à Gabaa, dans la campagne; ils tuèrent environ trente hommes d’Israël.
32 Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
Les fils de Benjamin disaient: « Les voilà battus devant nous comme auparavant! » Et les enfants d’Israël disaient: « Fuyons, et attirons-les loin de la ville, sur ces route. »
33 Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
Tous les hommes d’Israël quittèrent leur position et se rangèrent à Baal-Thamar; en même temps l’embuscade d’Israël s’élança de son poste, de la plaine de Gabaa.
34 Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
Dix mille hommes d’élite de tout Israël arrivèrent ainsi de devant Gabaa. Le combat fut rude, et les fils de Benjamin ne se doutaient pas que le malheur allait les atteindre.
35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
Yahweh battit Benjamin devant Israël, et les enfants d’Israël tuèrent ce jour-là à Benjamin vingt-cinq mille et cent hommes, tous tirant l’épée.
36 Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
Les fils de Benjamin virent donc qu’ils étaient battus. Les hommes d’Israël n’avaient, en effet, cédé du terrain à Benjamin que parce qu’ils avaient confiance dans l’embuscade qu’ils avaient placée contre Gabaa.
37 Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
Quant aux hommes de l’embuscade, ils se jetèrent promptement sur Gabaa; puis, s’avançant, les hommes de l’embuscade frappèrent toute la ville du tranchant de l’épée.
38 Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
Or il y avait ce signe convenu, entre les hommes d’Israël et ceux de l’embuscade. que ceux-ci feraient monter de la ville un nuage de fumée.
39 a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
Les hommes d’Israël firent alors volte-face dans la bataille. Les Benjamites leur avaient tué déjà environ trente hommes, et ils disaient: « Certainement les voilà battus devant nous comme dans le premier combat! »
40 Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
Mais le nuage commençait à s’élever de la ville comme une colonne de fumée, et les Benjamites, regardant derrière eux, aperçurent la ville entière qui montait en feu vers le ciel.
41 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
Les hommes d’Israël firent volte-face, et les hommes de Benjamin furent épouvantés en voyant que le malheur les atteignait.
42 Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
Ils tournèrent le dos devant les hommes d’Israël, par le chemin du désert; mais les combattants les serrèrent de prés, et ils tuèrent ceux des villes chacun en leurs propres endroits.
43 Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
Ils cernèrent Benjamin, ils le poursuivirent, ils l’écrasèrent là où il faisait halte, jusqu’en face de Gabaa, du côté du soleil levant.
44 Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
Il tomba dix-huit mille hommes de Benjamin, tous hommes vaillants.
45 Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
Ceux qui restaient tournèrent le dos et s’enfuirent vers le désert, vers le rocher de Remmon. Les hommes d’Israël tuèrent cinq mille hommes sur les routes; ils les serrèrent de près jusqu’à Gédéon, et ils en tuèrent deux mille.
46 A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
Le nombre total des Benjamites qui périrent ce jour-là fut de vingt-cinq mille hommes tirant l’épée, tous hommes vaillants.
47 Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
Six cents hommes qui avaient tourné le dos et s’étaient enfuis au désert, vers le rocher de Remmon, demeurèrent au rocher de Remmon pendant quatre mois.
48 Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.
Les hommes d’Israël revinrent vers les fils de Benjamin, et ils les frappèrent du tranchant de l’épée, depuis les villes, hommes et troupeaux, jusqu’à tout ce qu’on put trouver. Ils mirent aussi le feu à toutes les villes qu’ils trouvèrent.