< Mahukunta 20 >
1 Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
Alors tous les enfants d'Israël sortirent, et l'assemblée se rassembla comme un seul homme, depuis Dan jusqu'à Beer Schéba, avec le pays de Galaad, vers l'Éternel à Mitspa.
2 Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
Les chefs de tout le peuple, de toutes les tribus d'Israël, se présentèrent à l'assemblée du peuple de Dieu, quatre cent mille hommes de pied tirant l'épée.
3 (Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
(Les enfants de Benjamin apprirent que les enfants d'Israël étaient montés à Mitspa.) Les enfants d'Israël dirent: « Dis-nous, comment cette méchanceté est-elle arrivée? »
4 Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
Le Lévite, mari de la femme assassinée, répondit: « Je suis venu à Guibea, qui appartient à Benjamin, moi et ma concubine, pour passer la nuit.
5 Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
Les hommes de Guibea se sont soulevés contre moi et ont encerclé la maison pendant la nuit. Ils voulaient me tuer, ils ont violé ma concubine, et elle est morte.
6 Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
J'ai pris ma concubine, je l'ai coupée en morceaux, et je l'ai envoyée dans tout le pays de l'héritage d'Israël, car on s'est livré à la débauche et à la folie en Israël.
7 To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
Voici, vous, enfants d'Israël, vous tous, donnez ici vos avis et vos conseils. »
8 Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
Tout le peuple se leva comme un seul homme, et dit: Aucun de nous n'ira à sa tente, et aucun de nous ne se tournera vers sa maison.
9 Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
Voici maintenant ce que nous ferons à Guibea: nous monterons contre elle par le sort;
10 Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
et nous prendrons dix hommes sur cent dans toutes les tribus d'Israël, cent sur mille, et mille sur dix mille, pour procurer de la nourriture au peuple, afin qu'il fasse, en arrivant à Guibea de Benjamin, toutes les folies que les hommes de Guibea ont commises en Israël. »
11 Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
Et tous les hommes d'Israël se rassemblèrent contre la ville, unis comme un seul homme.
12 Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
Les tribus d'Israël envoyèrent des hommes dans toute la tribu de Benjamin, en disant: « Quelle est cette méchanceté qui est arrivée parmi vous?
13 Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
Maintenant, livrez les hommes, les méchants qui sont à Guibea, afin que nous les fassions mourir et que nous fassions disparaître le mal d'Israël. » Mais Benjamin ne voulut pas écouter la voix de ses frères, les enfants d'Israël.
14 Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
Les fils de Benjamin se rassemblèrent des villes jusqu'à Guibea, pour aller combattre les enfants d'Israël.
15 Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
Ce jour-là, on compta parmi les enfants de Benjamin, sur les villes, vingt-six mille hommes tirant l'épée, sans compter les habitants de Guibea, qui étaient au nombre de sept cents hommes d'élite.
16 Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
Parmi tous ces soldats, il y avait sept cents hommes d'élite qui étaient gauchers. Chacun d'eux pouvait lancer une pierre à un cheveu sans la manquer.
17 Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
Les hommes d'Israël, outre Benjamin, comptèrent quatre cent mille hommes tirant l'épée. Tous ces hommes étaient des hommes de guerre.
18 Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
Les enfants d'Israël se levèrent, montèrent à Béthel, et demandèrent conseil à Dieu. Ils demandèrent: « Qui montera le premier pour nous dans la bataille contre les enfants de Benjamin? » Yahvé a dit: « Juda d'abord. »
19 Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
Les enfants d'Israël se levèrent le matin et campèrent devant Guibea.
20 Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
Les hommes d'Israël sortirent pour combattre Benjamin, et les hommes d'Israël se rangèrent en bataille contre eux à Guibea.
21 Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
Les enfants de Benjamin sortirent de Guibea et, ce jour-là, ils détruisirent par terre vingt-deux mille hommes des Israélites.
22 Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
Le peuple, les hommes d'Israël, s'encouragèrent et se rangèrent en bataille à l'endroit où ils s'étaient rangés le premier jour.
23 Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
Les enfants d'Israël montèrent et pleurèrent devant l'Éternel jusqu'au soir, et ils demandèrent à l'Éternel: « M'approcherai-je encore pour combattre les enfants de Benjamin, mon frère? » Yahvé a dit: « Monte contre lui. »
24 Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
Les enfants d'Israël s'approchèrent des enfants de Benjamin le second jour.
25 A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
Benjamin sortit contre eux de Guibea, le second jour, et il détruisit encore par terre dix-huit mille hommes des enfants d'Israël. Tous tirèrent l'épée.
26 Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
Alors tous les enfants d'Israël et tout le peuple montèrent et vinrent à Béthel; ils pleurèrent, s'assirent là devant l'Éternel, et jeûnèrent ce jour-là jusqu'au soir; puis ils offrirent devant l'Éternel des holocaustes et des sacrifices de prospérité.
27 Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
Les enfants d'Israël demandèrent à l'Éternel (car l'arche de l'alliance de Dieu était là en ce temps-là,
28 Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
et Phinées, fils d'Éléazar, fils d'Aaron, se tenait devant elle en ce temps-là): « Irai-je encore combattre les enfants de Benjamin, mon frère, ou bien cesserai-je? » Yahvé dit: « Monte, car demain je le livrerai entre tes mains. »
29 Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
Israël dressa des embuscades tout autour de Guibea.
30 Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
Le troisième jour, les enfants d'Israël montèrent contre les enfants de Benjamin, et ils se rangèrent en bataille contre Guibea, comme les autres fois.
31 Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
Les Benjamites sortirent à l'encontre du peuple, et s'éloignèrent de la ville; ils se mirent à frapper et à tuer du peuple, comme les autres fois, sur les routes, dont l'une monte à Béthel et l'autre à Guibea, dans les champs, environ trente hommes d'Israël.
32 Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
Les fils de Benjamin dirent: « Ils sont frappés devant nous, comme au début. » Mais les enfants d'Israël dirent: « Fuyons, et attirons-les loin de la ville sur les routes. »
33 Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
Tous les hommes d'Israël se levèrent de leur place et se rangèrent en bataille devant Baal Tamar. Et les embusqueurs d'Israël sortirent de leur place, même de Maareh Guéba.
34 Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
Dix mille hommes d'élite de tout Israël s'avancèrent contre Guibea, et le combat fut rude; mais ils ne savaient pas que le désastre était proche d'eux.
35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
L'Éternel frappa Benjamin devant Israël, et les enfants d'Israël détruisirent ce jour-là vingt-cinq mille cent hommes de Benjamin. Tous tirèrent l'épée.
36 Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
Les fils de Benjamin virent qu'ils étaient frappés, car les hommes d'Israël avaient cédé à Benjamin parce qu'ils avaient confiance dans les embusqueurs qu'ils avaient placés contre Gibéa.
37 Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
Les embusqueurs se hâtèrent et se précipitèrent sur Gibéa; ils se répandirent et frappèrent toute la ville du tranchant de l'épée.
38 Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
Or le signe fixé entre les hommes d'Israël et les embusqueurs était de faire monter de la ville un grand nuage de fumée.
39 a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
Les hommes d'Israël se retournèrent dans la bataille, et Benjamin commença à frapper et à tuer environ trente personnes parmi les hommes d'Israël, car ils disaient: « Certainement ils ont été frappés devant nous, comme dans la première bataille. »
40 Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
Mais lorsque la nuée commença à s'élever de la ville en une colonne de fumée, les Benjamites regardèrent derrière eux, et voici que toute la ville montait en fumée vers le ciel.
41 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
Les hommes d'Israël se retournèrent, et les hommes de Benjamin furent consternés, car ils virent que le désastre les atteignait.
42 Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
Ils tournèrent le dos devant les hommes d'Israël pour prendre le chemin du désert, mais la bataille les suivit de près, et ceux qui sortirent des villes les détruisirent au milieu d'elles.
43 Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
Ils entourèrent les Benjamites, les poursuivirent et les foulèrent aux pieds sur leur lieu de repos, jusqu'aux environs de Guibea, vers le lever du soleil.
44 Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
Dix-huit mille hommes de Benjamin tombèrent; tous étaient des hommes valeureux.
45 Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
Ils se retournèrent et s'enfuirent vers le désert, au rocher de Rimmon. Ils en glanèrent cinq mille dans les chemins, les poursuivirent jusqu'à Gidom, et en battirent deux mille.
46 A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
Ainsi, tous ceux de Benjamin qui tombèrent ce jour-là furent vingt-cinq mille hommes qui tirèrent l'épée. Tous ceux-là étaient des hommes valeureux.
47 Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
Mais six cents hommes se détournèrent et s'enfuirent vers le désert, au rocher de Rimmon, et ils restèrent quatre mois au rocher de Rimmon.
48 Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.
Les hommes d'Israël se retournèrent contre les fils de Benjamin et les frappèrent du tranchant de l'épée, y compris toute la ville, le bétail et tout ce qu'ils trouvèrent. Ils incendièrent aussi toutes les villes qu'ils trouvèrent.