< Mahukunta 20 >
1 Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
And they went out all [the] people of Israel and it was assembled the congregation like a man one from Dan and to Beer Sheba and [the] land of Gilead to Yahweh Mizpah.
2 Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
And they presented themselves [the] corners of all the people all [the] tribes of Israel in [the] assembly of [the] people of God four hundred thousand man on foot [who] drew a sword.
3 (Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
And they heard [the] descendants of Benjamin that they had gone up [the] people of Israel Mizpah and they said [the] people of Israel speak how? did it occur the evil this.
4 Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
And he answered the man the Levite [the] husband of the woman murdered and he said Gibeah towards which [belongs] to Benjamin I came I and concubine my to spend [the] night.
5 Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
And they rose up on me [the] citizens of Gibeah and they surrounded on me the house night me they intended to kill and concubine my they abused and she died.
6 Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
And I took hold on concubine my and I cut in pieces her and I sent off her in all [the] land of [the] inheritance of Israel for they have done wickedness and disgraceful folly in Israel.
7 To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
Here! all of you O people of Israel give for yourselves a word and counsel here.
8 Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
And it arose all the people like a man one saying not we will go anyone to tent his and not we will depart anyone to house his.
9 Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
And now this [is] the thing which we will do to Gibeah on it by lot.
10 Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
And we will take ten men to the hundred of all - [the] tribes of Israel and one hundred to the thousand and one thousand to the ten thousand to bring provision[s] for the people to do to coming their to Geba of Benjamin according to all the disgraceful folly which it did in Israel.
11 Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
And it gathered every man of Israel to the city like a man one united.
12 Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
And they sent [the] tribes of Israel men in all [the] tribes of Benjamin saying what? [is] the evil this which it has happened among you.
13 Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
And therefore give up the men sons of worthlessness who [are] in Gibeah so we may put to death them and let us remove evil from Israel and not (they were willing [the] descendants *Q(K)*) of Benjamin to listen to [the] voice of brothers their [the] people of Israel.
14 Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
And they gathered [the] descendants of Benjamin from the cities Gibeah towards to go out for battle with [the] people of Israel.
15 Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
And they were mustered [the] descendants of Benjamin on the day that from the cities twenty and six thousand man [who] drew a sword apart from [the] inhabitants of Gibeah [who] they were mustered seven hundred man chosen.
16 Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
[were] from All - the people this seven hundred man chosen impeded [the] hand of right his all this [was] slinging with the stone to the single hair and not he missed.
17 Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
And [the] man of Israel they were mustered apart from Benjamin four hundred thousand man [who] drew a sword all this [was] man of war.
18 Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
And they arose and they went up Beth-el and they asked by God and they said [the] people of Israel who? will he go up for us at the first to the battle with [the] descendants of Benjamin and he said Yahweh Judah [will be] at the first.
19 Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
And they arose [the] people of Israel in the morning and they encamped on Gibeah.
20 Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
And he went out [the] man of Israel to the battle with Benjamin and they deployed with them [the] man of Israel battle to Gibeah.
21 Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
And they went out [the] descendants of Benjamin from Gibeah and they destroyed among Israel on the day that two and twenty thousand man [the] ground towards.
22 Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
And it showed itself strong the people [the] man of Israel and they repeated to deploy battle in the place where they had deployed there on the day first.
23 Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
And they went up [the] people of Israel and they wept before Yahweh until the evening and they enquired by Yahweh saying ¿ will I repeat to draw near for battle with [the] descendants of Benjamin brother my and he said Yahweh go up against him.
24 Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
And they drew near [the] people of Israel to [the] descendants of Benjamin on the day second.
25 A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
And it went out Benjamin - to meet them - from Gibeah on the day second and they destroyed among [the] people of Israel again eight-teen thousand man [the] ground towards all these [were] drawers of a sword.
26 Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
And they went up all [the] people of Israel and all the people and they came Beth-el and they wept and they sat there before Yahweh and they fasted on the day that until the evening and they offered up burnt offerings and peace offerings before Yahweh.
27 Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
And they enquired [the] people of Israel by Yahweh and [was] there [the] ark of [the] covenant of God in the days those.
28 Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
And Phinehas [the] son Eleazar [the] son of Aaron [was] standing - before it in the days those saying ¿ will I repeat again to go out for battle with [the] descendants of Benjamin brother my or? will I cease and he said Yahweh go up for tomorrow I will give him in hand your.
29 Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
And it set Israel ambushers to Gibeah round about.
30 Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
And they went up [the] people of Israel against [the] descendants of Benjamin on the day third and they deployed against Gibeah as time on time.
31 Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
And they went out [the] descendants of Benjamin to meet the people they were drawn away from the city and they began to strike down some of the people fatally wounded as time - on time in the highways which one [is] going up Beth-el and one Gibeah towards in the field about thirty man in Israel.
32 Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
And they said [the] descendants of Benjamin [are] defeated they before us as at the former [time] and [the] people of Israel they said let us flee and we will draw away him from the city to the highways.
33 Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
And every - man of Israel they rose from place his and they deployed at Baal Tamar and [the] ambusher of Israel [was] bursting forth from place his from [the] open place of Geba.
34 Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
And they came from before to Gibeah ten thousand man chosen from all Israel and the battle it was heavy and they not they knew that [was] about to touch to them calamity.
35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
And he defeated Yahweh - Benjamin before Israel and they destroyed [the] people of Israel among Benjamin on the day that twenty and five thousand and one hundred man all these [was] drawing a sword.
36 Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
And they saw [the] descendants of Benjamin for they were defeated and they gave [the] man of Israel place to Benjamin for they trusted to the ambusher whom they had set against Gibeah.
37 Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
And the ambusher they made haste and they made a raid against Gibeah and he marched the ambusher and he struck all the city to [the] mouth of [the] sword.
38 Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
And the appointed signal it belonged to [the] man of Israel with the ambusher make great to cause to go up they [the] rising of the smoke from the city.
39 a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
And he turned [the] man of Israel in the battle and Benjamin it began to strike down fatally wounded among [the] man of Israel about thirty man for they said surely certainly [is] defeated it before us like the battle first.
40 Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
And the rising it began to go up from the city a pillar of smoke and it turned Benjamin behind it and there! it went up [the] entirety of the city the heavens towards.
41 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
And [the] man of Israel he turned and he was terrified [the] man of Benjamin if he saw that it had touched to him calamity.
42 Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
And they turned before [the] man of Israel to [the] way of the wilderness and the battle it overtook him and [those] who [were] from the cities [were] destroying him in [the] midst of him.
43 Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
They surrounded Benjamin they pursued him rest they trod down him to opposite Gibeah from [the] rising of [the] sun.
44 Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
And they fell of Benjamin eight-teen thousand man all these [were] men of strength.
45 Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
And they turned and they fled the wilderness towards to [the] rock of Rimmon and they gleaned him in the highways five thousand man and they pursued closely after him to Gidom and they struck down of him two thousand man.
46 A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
And it was all those [who] fell of Benjamin twenty and five thousand man [who] drew a sword on the day that all these [were] men of strength.
47 Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
And they turned and they fled the wilderness towards to [the] rock of Rimmon six hundred man and they dwelt at [the] rock of Rimmon four months.
48 Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.
And [the] man of Israel they turned back against [the] descendants of Benjamin and they struck them to [the] mouth of [the] sword from a city of soundness unto animal unto everything which was found also all the cities which were found they sent in fire.