< Mahukunta 20 >

1 Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
Then went forth all the sons of Israel, and the assembly came together as one man, from Dan even to Beersheba with the land of Gilead, —unto Yahweh at Mizpah.
2 Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
And the chiefs of all the people—all the tribes of Israel—presented themselves in the convocation of the people of God, —four hundred thousand footmen, that drew the sword.
3 (Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
And the sons of Benjamin heard that the sons of Israel had gone up to Mizpah. Then said the sons of Israel, Tell [us], In what manner was brought to pass this vileness?
4 Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
And the Levite, husband of the woman that was cut in pieces, responded and said, —Into Gibeah that pertaineth to Benjamin, I entered, I and my concubine, to tarry the night.
5 Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
And the owners of Gibeah rose up against me, and beset the house, for my sake, by night, —me, they thought to slay, and, my concubine, they so humbled, that she died.
6 Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
So I laid hold on my concubine, and cut her in pieces, and sent her throughout all the country of the inheritance of Israel, —because they had wrought lewdness and impiety, in Israel.
7 To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
Lo! ye all, are sons of Israel, —give your word and counsel, here.
8 Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
Then arose all the people, as one man, saying, —No man of us will go to his tent, and no man of us will turn aside to his house.
9 Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
Now, therefore, this is the thing, that we will do to Gibeah, —[Go] against it by lot;
10 Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
and we will take ten men of a hundred, of all the tribes of Israel, and a hundred of a thousand, and a thousand of ten thousand, to fetch provisions for the people, —that they may do, when they come to Gibeah of Benjamin, according to all the impiety that it hath wrought in Israel.
11 Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
So all the men of Israel were gathered together against the city, as one man knit together.
12 Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
And the tribes of Israel sent men throughout all the divisions of Benjamin, saying, —What is this vile thing that hath been brought to pass, among you?
13 Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
Now, therefore, deliver up the men—the sons of the Abandoned One—who are in Gibeah, that we may put them to death, and vileness be consumed out of Israel. But [the sons of] Benjamin would not hearken unto the voice of their brethren, the sons of Israel.
14 Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
Then did the sons of Benjamin gather themselves together out of the cities, unto Gibeah, —to go forth to battle against the sons of Israel.
15 Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
And the sons of Benjamin were numbered on that day, out of the cities, twenty-six thousand men, that drew the sword, —besides, of the inhabitants of Gibeah, were numbered seven hundred chosen men.
16 Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
Out of all this people, were seven hundred chosen men, left-handed, —any one of whom could sling with a stone to a hair’s-breadth, and not miss.
17 Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
And, the men of Israel, were numbered, apart from Benjamin, four hundred thousand men, that drew the sword, —every one of these being a man of war.
18 Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
And they arose, and went up to Bethel, and asked of God, and the sons of Israel said, Who shall go up for us first, to fight against the sons of Benjamin? And Yahweh said—Judah, first.
19 Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
And the sons of Israel arose in the morning, —and encamped against Gibeah.
20 Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
And the men of Israel went forth, to fight against Benjamin, —so the men of Israel set themselves in array against them, to fight against Gibeah.
21 Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
Then came forth the sons of Benjamin out of Gibeah, —and laid low of Israel, on that day, twenty-two thousand men, to the ground.
22 Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
And the people, the men of Israel, encouraged themselves, —and again set themselves in array for battle in the place where they had set themselves in array on the first day.
23 Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
Now the sons of Israel had gone up, and wept before Yahweh, until the evening, and asked of Yahweh, saying, Shall I again draw near to battle against the sons of Benjamin, my brother? And Yahweh said, Go up against him.
24 Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
So the sons of Israel came near against the sons of Benjamin, on the second day.
25 A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
And Benjamin came forth to meet them out of Gibeah, on the second day, and laid low, of the sons of Israel, yet eighteen thousand men, to the ground, —all these, drew the sword.
26 Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
Then went up all the sons of Israel, and all the people, and came to Bethel, and wept, and tarried there before Yahweh, and fasted on that day, until the evening, —and caused to go up ascending-sacrifices and peace-offerings, before Yahweh.
27 Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
And the sons of Israel asked of Yahweh, —there, being the ark of the covenant of God, in those days;
28 Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
and Phinehas, son of Eleazar, son of Aaron, was standing before it in those days, saying: Shall I yet again go forth to battle, against the sons of Benjamin, my brother, or shall I forbear? And Yahweh said—Go up, for, to-morrow, will I deliver him into thy hand.
29 Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
And Israel set liers in wait against Gibeah, round about.
30 Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
So the sons of Israel went up against the sons of Benjamin, on the third day, —and set themselves in array against Gibeah, as time after time.
31 Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
And the sons of Benjamin came forth against the people, they were drawn away from the city, —and began to smite of the people, slaying as time after time, in the highways, whereof, one, goeth up to Bethel, and, the other, to Gibeah in the field, about thirty men in Israel.
32 Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
Then said the sons of Benjamin, They are, being smitten, before us, as at the first. But the sons of Israel had said—Let us flee, and draw them away from the city, into the highways.
33 Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
And, all the men of Israel, rose up out of their place, and set themselves in array in Baal-tamar, —and, the liers in wait of Israel, began to break forth out of their place, out of the forest of Gibeah.
34 Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
And there came over against Gibeah ten thousand chosen men, out of all Israel, and the battle was severe, —they, not knowing that disaster was overtaking them.
35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
Thus Yahweh smote Benjamin before Israel, and the sons of Israel destroyed in Benjamin, that day, twenty-five thousand and one hundred men, —all these, drew the sword.
36 Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
So the sons of Benjamin saw that they were smitten, —and that the men of Israel had given place to Benjamin, because they trusted to the liers in wait, whom they had set near Gibeah.
37 Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
And, the liers in wait, hasted, and rushed upon Gibeah, —and the liers in wait marched forward, and smote all the city with the edge of the sword.
38 Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
Now, the appointed sign, between the men of Israel and the liers in wait, had been, —to cause a great cloud of smoke to ascend out of the city.
39 a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
So, when the men of Israel turned in the battle, —and, the Benjamites, began to smite and slay of the sons of Israel, about thirty men, for they said, Yea! they are, smitten, before us, as in the first battle,
40 Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
then, the cloud, began to ascend out of the city, a pillar of smoke, —and the Benjamites looked behind them, and lo! the whole city flamed up towards the heavens.
41 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
And, when, the men of Israel, turned, then were the men of Benjamin dismayed, —for they saw that disaster had overtaken them.
42 Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
And, when they turned before the men of Israel unto the way of the desert, the battle, over took them, —while, as for them that came out of the cities, they began to destroy them in their midst: —
43 Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
they hemmed in the Benjamites, they pursued them, with ease, trode they them down, —as far as over against Gibeah, towards sunrise.
44 Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
So there fell of Benjamin, eighteen thousand men, —all these being men of valour.
45 Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
And, when they turned and fled towards the desert unto the cliff Rimmon, then gleaned they of them, in the highways, five thousand men, —and they followed hard after them as far as Gidom, and smote of them, two thousand men.
46 A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
So then it came to pass that, all the fallen of Benjamin, were twenty-five thousand men, that drew the sword, on that day, —all these being men of valour.
47 Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
But there turned and fled, towards the desert, unto the cliff Rimmon, six hundred men, —who abode in the cliff Rimmon, four months.
48 Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.
Thus, the men of Israel, turned against the sons of Benjamin, and smote them with the edge of the sword, beginning with the city, each and every one down to the beast, even to every one that was met with, —moreover, all the cities they came to, they set on fire.

< Mahukunta 20 >