< Mahukunta 20 >

1 Sa’an nan dukan Isra’ilawa daga Dan zuwa Beyersheba kuma daga ƙasar Gileyad mutane kamar mutum guda suka fito suka taru a gaban Ubangiji a Mizfa.
Then all the children of Israel went out, and the Congregation was gathered together as one man, from Dan to Beersheba, with the land of Gilead, vnto the Lord in Mizpeh.
2 Shugabanni dukan kabilan mutane na kabilan Isra’ila suka zazzauna a wurarensu a taron jama’ar Allah, mayaƙa dubu ɗari huɗu masu ɗamara da takuba.
And the chiefe of all the people, and all the tribes of Israel assembled in the Congregation of the people of God foure hundreth thousand footemen that drewe sword.
3 (Mutanen Benyamin suka ji cewa Isra’ilawa sun haura zuwa Mizfa.) Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Gaya mana yadda wannan mugun abu ya faru.”
(Now the children of Beniamin heard that the children of Israel were gone vp to Mizpeh) Then the children of Israel saide, Howe is this wickednesse committed?
4 Sai Balawen, mijin matar da aka kashe ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata mun zo Gibeya a Benyamin don mu kwana.
And the same Leuite, the womans husband that was slaine, answered and saide, I came vnto Gibeah that is in Beniamin with my concubine to lodge,
5 Da dad dare mutanen Gibeya suka bi ni suka kewaye gidan da niyya su kashe ni. Suka yi wa ƙwarƙwarata fyaɗe, har ta mutu.
And the men of Gibeah arose against me, and beset the house round about vpon mee by night, thinking to haue slaine me, and haue forced my concubine that she is dead.
6 Na ɗauki ƙwarƙwarata na yayyanka gunduwa-gunduwa na aika da shi ga kowane yankin gādon Isra’ila, domin sun aikata mugu abu da abin kunya a Isra’ila.
Then I tooke my concubine, and cut her in pieces, and sent her throughout all the countrey of the inheritance of Israel: for they haue committed abomination and villenie in Israel.
7 To, dukanku Isra’ilawa, sai ku yi magana ku kuma yanke hukuncinku.”
Behold, ye are al children of Israel: giue your aduise, and counsell herein.
8 Dukan mutane suka tashi kamar mutum ɗaya, suna cewa “Ba waninmu da zai tafi gida. Sam, babu ko ɗayanmu da zai koma gidansa.
Then all the people arose as one man, saying, There shall not a man of vs goe to his tent, neither any turne into his house.
9 Amma yanzu ga abin da za mu yi wa Gibeya. Za mu haura mu fāɗa yadda ƙuri’a ta nunar.
But now this is that thing which we will do to Gibeah: we wil goe vp by lot against it,
10 Za mu ɗauko mutum goma a kowane mutum ɗari daga dukan kabilan Isra’ila, da ɗari a dubu, da kuma dubu a dubu goma, domin a tanada wa mayaƙan. Sa’an nan, sa’ad da mayaƙan suka iso Geba a Benyamin, za su yi da su daidai bisa ga muguntar da suka yi a Isra’ila.”
And we wil take ten men of the hundreth throughout al the tribes of Israel, and an hundreth of the thousand, and a thousand of ten thousand to bring vitaile for the people that they may do (when they come to Gibeah of Beniamin) according to all the villeny, that it hath done in Israel.
11 Saboda haka dukan mutane Isra’ilawa suka taru suka kuma haɗu kamar mutum guda don su fāɗa wa birnin da yaƙi.
So all the men of Israel were gathered against the citie, knit together, as one man.
12 Kabilan Isra’ila suka aika jakadu a ko’ina a cikin kabilar Benyamin cewa, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata?
And the tribes of Israel sent men through al the tribe of Beniamin, saying, What wickednesse is this that is committed among you?
13 Yanzu fa sai ku fitar da waɗannan’yan iskan da suka aikata wannan abu na Gibeya don mu kashe su mu kawar da mugunta daga Isra’ila!” Amma mutanen Benyamin ba su saurari’yan’uwansu Isra’ilawa ba.
Nowe therefore deliuer vs those wicked men which are in Gibeah, that we may put them to death, and put away euill from Israel: but the children of Beniamin would not obey the voyce of their brethren the children of Israel.
14 Daga biranensu suka tattaru a Gibeya don su yaƙi Isra’ilawa.
But ye children of Beniamin gathered them selues together out of the cities vnto Gibeah, to come out and fight against the children of Israel.
15 Nan da nan mutanen Benyamin suka tattara mayaƙa dubu ashirin da shida masu takuba daga biranensu, ban da mayaƙa ɗari bakwai da aka zaɓa daga mazauna a Gibeya.
And ye children of Beniamin were nombred at that time out of the cities sixe and twenty thousand men that drewe sworde, beside the inhabitants of Gibeah, which were nombred seuen hundreth chosen men.
16 Cikin dukan mayaƙan nan akwai zaɓaɓɓu mutane ɗari bakwai waɗanda su bahagwai ne, kowanne yana iya harbin gashin guda na kai da majajjawa ba kuskure.
Of all this people were seuen hundreth chosen men, being left handed: all these could sling stones at an heare breadth, and not faile.
17 Isra’ila kuwa, ban da Benyamin, sun tara mayaƙa masu takobi dubu ɗari huɗu, dukansu gwanayen yaƙi ne.
Also the men of Israel, beside Beniamin, were nombred foure hundreth thousande men that drew sword, euen all men of warre.
18 Sai Isra’ilawa suka haura zuwa Betel suka nemi nufin Allah, suka ce, “Wane ne a cikinmu zai fara fāɗa wa mutanen Benyamin?” Ubangiji ya ce, “Yahuda ce za tă fara.”
And the children of Israel arose, and went vp to the house of God, and asked of God, saying, Which of vs shall goe vp first to fight against the children of Beniamin? And the Lord said, Iudah shalbe first.
19 Kashegari sai Isra’ilawa suka tashi suka kafa sansani kusa da Gibeya.
Then the children of Israel arose vp earely and camped against Gibeah.
20 Mutanen Isra’ila suka fita yaƙi da mutane Benyamin suka kuma ja dāgār yaƙi a Gibeya.
And the men of Israel went out to battell against Beniamin, and the men of Israel put themselues in aray to fight against the beside Gibeah.
21 Mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya suka kashe mutum dubu ashirin da biyu na Isra’ilawa a dāgār yaƙi a ranar.
And the children of Beniamin came out of Gibeah, and slewe downe to the ground of the Israelites that day two and twentie thousand men.
22 Amma mutanen Isra’ila suka ƙarfafa juna, suka sāke koma inda suka ja dāgā a rana ta farko.
And the people, the men of Israel plucked vp their hearts, and set their battel againe in aray in the place where they put them in aray the first day.
23 Isra’ilawa suka haura suka yi kuka a gaban Ubangiji, har yamma, suka nemi nufin Ubangiji. Suka ce, “Mu sāke koma yaƙi da mutanen Benyamin,’yan’uwanmu?” Ubangiji ya ce, “Ku haura ku fāɗa musu.”
(For the children of Israel had gone vp and wept before the Lord vnto the euening, and had asked of the Lord, saying, Shall I goe againe to battel against the children of Beniamin my brethren? and the Lord said, Go vp against them)
24 Sai Isra’ilawa suka matsa kusa da Benyamin a rana ta biyu.
Then the children of Israel came neere against the children of Beniamin the second day.
25 A wannan lokaci, da mutanen Benyamin suka fito daga Gibeya don su yaƙe su, sai suka sāke kashe Isra’ilawa dubu goma sha takwas, dukansu ɗauke da takuba.
Also the second day Beniamin came forth to meete them out of Gibeah, and slewe downe to the grounde of the children of Israel againe eighteene thousand men: all they could handle the sword.
26 Sa’an nan Isra’ilawa, dukan mutane, suka haura zuwa Betel, a can suka zauna suna kuka a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a wannan rana har yamma suka miƙa hadayun ƙonawa da hadayun salama ga Ubangiji.
Then al the children of Israel went vp and all the people came also vnto the house of God, and wept and sate there before the Lord and fasted that day vnto the euening, and offred burnt offrings and peace offrings before the Lord.
27 Isra’ilawa suka nemi nufin Ubangiji (A kwanakin nan akwatin alkawarin Allah yana can,
And the children of Israel asked the Lord (for there was the Arke of the couenat of God in those dayes,
28 Finehas ɗan Eleyazar, ɗan Haruna, kuwa yana hidima a gabansa.) Suka ce, “Mu sāke haura mu yi yaƙi da mutanen Benyamin’yan’uwanmu, ko a’a?” Ubangiji ya ce, “Ku je, gama gobe zan ba da su a hannuwanku.”
And Phinehas the sonne of Eleazar, the sonne of Aaron stoode before it at that time) saying, Shall I yet goe anie more to battel against the children of Beniamin my brethren, or shall I cease? And the Lord said, Go vp: for to morowe I will deliuer them into your hand.
29 Sa’an nan Isra’ila ta yi kwanto kewaya da Gibeya.
And Israel set men to lie in waite round about Gibeah.
30 Suka haura su kara da mutanen Benyamin a rana ta uku suka ja dāgā a Gibeya kamar dā.
And the children of Israel went vp against the children of Beniamin the third day, and put theselues in aray against Gibeah, as at other times.
31 Mutanen Benyamin suka fito su same su aka kuma jawo su nesa da birnin. Suka fara karkashe Isra’ilawa kamar dā, har aka kashe wajen mutum talatin a filaye da kuma a hanyoyi, wadda take zuwa Betel da kuma wadda take zuwa Gibeya.
Then the children of Beniamin comming out against the people, were drawen from the citie: and they began to smite of ye people and kill as at other times, euen by the wayes in the fielde (whereof one goeth vp to the house of God, and the other to Gibeah) vpon a thirtie men of Israel.
32 Yayinda mutanen Benyamin suna cewa, “Muna cin nasara a kansu kamar dā,” Isra’ilawa kuwa suna cewa, “Mu yi ta jan da baya mu janye su daga birni zuwa kan hanyoyi.”
(For the children of Beniamin sayd, They are fallen before vs, as at the first. But the children of Israel saide, Let vs flee and plucke them away from the citie vnto the hie wayes)
33 Dukan mutanen Isra’ila suka taso daga wurarensu suka ja dāgā a Ba’al-Tamar, Isra’ilawan da suka yi kwanto a yammancin Geba kuwa suka fito.
And all the men of Israel rose vp out of their place, and put themselues in aray at Baal-tamar: and the men that lay in wayte of the Israelites came forth of their place, euen out of the medowes of Gibeah,
34 Sa’an nan jarumai Isra’ila dubu goma suka yi gaba suka kai wa Gibeya hari. Yaƙi kuwa ya yi zafi har mutane Benyamin ba su san masifa tana dab da su ba.
And they came ouer against Gibeah, ten thousande chosen men of all Israel, and the battell was sore: for they knewe not that the euill was neere them.
35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Benyamin a gaban Isra’ila; a ranar kuwa Isra’ilawa sun kashe mutum 25,100 na mutanen Benyamin, dukansu ɗauke da takuba.
And the Lord smote Beniamin before Israel, and the children of Israel destroyed of the Beniamites the same day fiue and twenty thousand and an hundreth men: all they could handle the sword.
36 Sa’an nan Benyamin suka ga an ci su. To, mutanen Isra’ila sun yi ta ja da baya daga mutanen Benyamin domin suna dogara ga waɗanda sa su yi kwanto kusa da Gibeya ne.
So the children of Beniamin sawe that they were striken downe: for the men of Israel gaue place to the Beniamites, because they trusted to the men that lay in waite, which they had laide beside Gibeah.
37 Mutanen da suke kwanto suka yi wuf suka ruga cikin Gibeya, suka bazu suka kuma karkashe dukan waɗanda suke a birnin.
And they that lay in wait hasted, and brake forth toward Gibeah, and the ambushment drewe themselues along, and smote all the citie with the edge of the sword.
38 Mutanen Isra’ila sun riga sun shirya da’yan kwanton cewa su murtuke hayaƙi daga birnin,
Also the men of Israel had appoynted a certaine time with the ambushmentes, that they should make a great flame and smoke rise vp out of the citie.
39 a sa’an nan ne mutanen Isra’ila za su juya su fāɗa wa mutane Benyamin da yaƙi. Mutanen Benyamin sun fara karkashe mutum talatin na Isra’ila, sai suka ce, “Muna cin nasara a kansu kamar dā.”
And when the men of Israel retired in the battel, Beniamin began to smite and kill of the men of Israel about thirtie persons: for they said, Surely they are striken downe before vs, as in the first battell.
40 Amma da alamar hayaƙi ya fara murtukewa daga birnin, sai mutanen Benyamin suka juya suka ga hayaƙi yana murtukewa ko’ina a cikin birnin zuwa sararin sama.
But when the flame bega to arise out of the citie, as a pillar of smoke, the Beniamites looked backe, and behold, the flame of the citie began to ascend vp to heauen.
41 Sa’an nan mutanen Isra’ila suka juyo musu, mutanen Benyamin kuwa suka tsorata domin sun gane masifa ta zo musu.
Then the men of Israel turned againe, and the men of Beniamin were astonied: for they saw that euill was neere vnto them.
42 Saboda haka suka tsere a gaban Isra’ila zuwa wajen hamada, amma ba su iya tsere wa yaƙin ba. Mutanen Isra’ila da suka fito daga cikin birnin suka karkashe su a can.
Therefore they fled before the men of Israel vnto the way of the wildernesse, but the battell ouertooke them: also they which came out of the cities, slew them among them.
43 Suka kewaye mutanen Benyamin, suka kore su, suka fatattake su a wajajen Gibeya a gabashi.
Thus they compassed the Beniamites about, and chased them at ease, and ouerranne them, euen ouer against Gibeah on the Eastside.
44 Mutum dubu goma sha takwas na mutanen Benyamin suka mutu dukansu kuwa jarumai ne.
And there were slaine of Beniamin eyghteene thousad men, which were all men of warre.
45 Da suka juya suka juya suka tsere zuwa wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, Isra’ilawa suka kashe mutum dubu biyar a kan hanyoyi. Suka yi ta matsa wa mutanen Benyamin har zuwa Gidom suka kashe mutum dubu biyu kuma.
And they turned and fled to the wildernes vnto the rocke of Rimmon: and the Israelites glayned of them by the way fiue thousand men, and pursued after them vnto Gidom, and slewe two thousand men of them,
46 A ranar kuwa mutanen Benyamin dubu ashirin da biyar ne aka kashe, dukansu jarumai.
So that all that were slayne that day of Beniamin, were fiue and twentie thousand men that drewe sword, which were all men of warre:
47 Amma mutane ɗari shida suka juya suka tsere wajajen hamada zuwa dutsen Rimmon, inda suka zauna wata huɗu.
But sixe hundreth men turned and fled to the wildernesse vnto the rocke of Rimmon, and abode in the rocke of Rimmon foure moneths.
48 Mutanen Isra’ila suka koma wurin mutanen Benyamin suka kashe dukan waɗanda suke a birnin, tare da dabbobi da kome da suka samu. Dukan garuruwan da suka samu sun ƙone su ƙaf.
Then the men of Israel returned vnto the children of Beniamin, and smote them with the edge of the sword from the men of the citie vnto the beasts, and all that came to hand: also they set on fire all the cities that they coulde come by.

< Mahukunta 20 >