< Mahukunta 2 >

1 Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
Gospodov angel je prišel gor od Gilgála k Bohímu in rekel: »Primoral sem vas iti gor, ven iz Egipta in vas privedel v deželo, ki sem jo prisegel vašim očetom. Rekel sem: ›Nikoli ne bom prelomil svoje zaveze z vami.
2 ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
In vi ne boste sklenili nobene zaveze s prebivalci te dežele; zrušili boste njihove oltarje.‹ Toda niste ubogali mojega glasu. Zakaj ste to storili?‹
3 Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
Zato sem tudi rekel: ›Ne bom jih pognal izpred vas, temveč vam bodo kakor trni na vaših straneh in njihovi bogovi vam bodo zanka.‹«
4 Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
Pripetilo se je, ko je Gospodov angel te besede povedal vsem Izraelovim otrokom, da je ljudstvo povzdignilo svoj glas in zajokalo.
5 sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
Ime tega kraja so imenovali Bohím in tam so darovali Gospodu.
6 Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
Ko je Józue pustil ljudstvu oditi, so Izraelovi otroci odšli, vsak mož v svojo dediščino, da deželo vzamejo v last.
7 Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
Ljudstvo je služilo Gospodu vse Józuetove dni in vse dni starešin, ki so preživeli Józueta, ki so videli vsa velika Gospodova dela, ki jih je storil za Izrael.
8 Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
Nunov sin Józue, Gospodov služabnik, je umrl, star sto deset let.
9 Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
Pokopali so ga na meji njegove dediščine, v Timnát Heresu, na gori Efrájim, na severni strani Gáaševega hriba.
10 Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
Tudi ves ta rod je bil zbran k svojim očetom in tam je za njimi vstal drug rod, ki ni poznal Gospoda niti še ne del, ki jih je ta storil za Izrael.
11 Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
Izraelovi otroci so počeli zlo v Gospodovih očeh in služili Báalom.
12 Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
Zapustili so Gospoda, Boga svojih očetov, ki jih je privedel iz egiptovske dežele in sledili drugim bogovom, bogovom ljudstev, ki so bili okoli njih, se jim priklanjali in Gospoda izzivali k jezi.
13 domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
Zapustili so Gospoda in služili Báalu in Astarti.
14 Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
Gospodova jeza je bila vroča zoper Izrael in izročil jih je v roke plenilcev, ki so jih oplenili in jih prodal v roke njihovih sovražnikov naokoli, tako da ne bi mogli več obstati pred svojimi sovražniki.
15 Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
Kamorkoli so odšli, je bila zoper njih Gospodova roka za zlo, kakor je Gospod rekel in kakor jim je Gospod prisegel. Bili so silno stiskani.
16 Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
Kljub temu je Gospod dvignil sodnike, ki so jih osvobajali iz roke tistih, ki so jih plenili.
17 Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
Vendar niso hoteli prisluhniti svojim sodnikom, temveč so se odšli vlačugat za drugimi bogovi in se jim priklanjali. Hitro so se obrnili iz poti, po kateri so hodili njihovi očetje z uboganjem Gospodovih zapovedi, toda oni niso tako storili.
18 Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
Ko jim je Gospod dvignil sodnike, potem je bil Gospod s sodnikom in jih vse sodnikove dni osvobajal iz roke njihovih sovražnikov, kajti to je pokesalo Gospoda zaradi njihovega stokanja, zaradi razloga tistih, ki so jih zatirali in jih slabili.
19 Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
Pripetilo pa se je, ko je bil sodnik mrtev, da so se vrnili in se izpridili bolj kakor njihovi očetje v sledenju drugim bogovom, da jim služijo in se jim priklanjajo. Niso odnehali od svojih lastnih početij niti od svoje trmoglave poti.
20 Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
Gospodova jeza je bila vroča zoper Izrael in rekel je: »Zato, ker je to ljudstvo prekršilo mojo zavezo, ki sem jo zapovedal njihovim očetom in niso prisluhnili mojemu glasu,
21 ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
odslej tudi jaz pred njimi ne bom podil kateregakoli izmed narodov, ki jih je pustil Józue, ko je umrl,
22 Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
da bom lahko po njih preizkusil Izraela, če se bodo držali Gospodove poti, da hodijo po njej, kakor so se je držali njihovi očetje ali ne.«
23 Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.
Zato je Gospod pustil tiste narode, ne da bi jih naglo pognal ven niti jih ni izročil v Józuetovo roko.

< Mahukunta 2 >