< Mahukunta 2 >

1 Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
و فرشته خداوند از جلجال به بوکیم آمده، گفت: «شما را از مصر برآوردم و به زمینی که به پدران شما قسم خوردم داخل کردم، و گفتم عهد خود را با شما تا به ابد نخواهم شکست.۱
2 ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
پس شما با ساکنان این زمین عهد مبندید ومذبح های ایشان را بشکنید، لیکن شما سخن مرانشنیدید. این چه‌کار است که کرده‌اید؟۲
3 Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
لهذا من نیز گفتم ایشان را از حضور شما بیرون نخواهم کرد، و ایشان در کمرهای شما خارها خواهندبود، و خدایان ایشان برای شما دام خواهند بود.»۳
4 Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
و چون فرشته خداوند این سخنان را به تمامی اسرائیل گفت، قوم آواز خود را بلند کرده، گریستند.۴
5 sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
و آن مکان را بوکیم نام نهادند، و درآنجا برای خداوند قربانی گذرانیدند.۵
6 Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
و چون یوشع قوم را روانه نموده بود، بنی‌اسرائیل هر یکی به ملک خود رفتند تا زمین رابه تصرف آورند.۶
7 Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
و در تمامی ایام یوشع و تمامی ایام مشایخی که بعد از یوشع زنده ماندند، و همه کارهای بزرگ خداوند را که برای اسرائیل کرده بود، دیدند، قوم، خداوند را عبادت نمودند.۷
8 Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
ویوشع بن نون، بنده خداوند، چون صد و ده ساله بود، مرد.۸
9 Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
و او را در حدود ملکش در تمنه حارس در کوهستان افرایم به طرف شمال کوه جاعش دفن کردند.۹
10 Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
و تمامی آن طبقه نیز به پدران خودپیوستند، و بعد از ایشان طبقه دیگر برخاستند که خداوند و اعمالی را که برای اسرائیل کرده بود، ندانستند.۱۰
11 Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
و بنی‌اسرائیل در نظر خداوند شرارت ورزیدند، و بعلها را عبادت نمودند.۱۱
12 Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
و یهوه خدای پدران خود را که ایشان را از زمین مصربیرون آورده بود، ترک کردند، و خدایان غیر را ازخدایان طوایفی که در اطراف ایشان بودند پیروی نموده، آنها را سجده کردند. و خشم خداوند رابرانگیختند.۱۲
13 domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
و یهوه را ترک کرده، بعل وعشتاروت را عبادت نمودند.۱۳
14 Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
پس خشم خداوند بر اسرائیل افروخته شده، ایشان را به‌دست تاراج کنندگان سپرد تا ایشان را غارت نمایند، و ایشان را به‌دست دشمنانی که به اطراف ایشان بودند، فروخت، به حدی که دیگرنتوانستند با دشمنان خود مقاومت نمایند.۱۴
15 Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
و به هرجا که بیرون می‌رفتند، دست خداوند برای بدی بر ایشان می‌بود، چنانکه خداوند گفته، و چنانکه خداوند برای ایشان قسم خورده بود و به نهایت تنگی گرفتار شدند.۱۵
16 Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
و خداوند داوران برانگیزانید که ایشان را ازدست تاراج کنندگان نجات دادند.۱۶
17 Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
و باز داوران خود را اطاعت ننمودند، زیرا که در عقب خدایان غیر زناکار شده، آنها را سجده کردند، و از راهی که پدران ایشان سلوک می‌نمودند، و اوامرخداوند را اطاعت می‌کردند، به زودی برگشتند، و مثل ایشان عمل ننمودند.۱۷
18 Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
و چون خداوندبرای ایشان داوران برمی انگیخت خداوند با داورمی بود، و ایشان را در تمام ایام آن داور از دست دشمنان ایشان نجات می‌داد، زیرا که خداوند به‌خاطر ناله‌ای که ایشان از دست ظالمان وستم کنندگان خود برمی آوردند، پشیمان می‌شد.۱۸
19 Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
و واقع می‌شد چون داور وفات یافت که ایشان برمی گشتند و از پدران خود بیشتر فتنه انگیز شده، خدایان غیر را پیروی می‌کردند، و آنها را عبادت نموده، سجده می‌کردند، و از اعمال بد و راههای سرکشی خود چیزی باقی نمی گذاشتند.۱۹
20 Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
لهذاخشم خداوند بر اسرائیل افروخته شد و گفت: «چونکه این قوم از عهدی که با پدران ایشان امرفرمودم، تجاوز نموده، آواز مرا نشنیدند،۲۰
21 ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
من نیز هیچ‌یک از امتها را که یوشع وقت وفاتش واگذاشت، از حضور ایشان دیگر بیرون نخواهم نمود.۲۱
22 Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
تا اسرائیل را به آنها بیازمایم که آیاطریق خداوند را نگهداشته، چنانکه پدران ایشان نگهداشتند، در آن سلوک خواهند نمود یا نه.»۲۲
23 Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.
پس خداوند آن طوایف را واگذاشته، به‌سرعت بیرون نکرد و آنها را به‌دست یوشع تسلیم ننمود.۲۳

< Mahukunta 2 >