< Mahukunta 2 >
1 Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
Og Herrens engel kom fra Gilgal op til Bokim. Og han sa: Jeg hentet eder op fra Egypten og førte eder til det land jeg tilsvor eders fedre, og sa: Aldri i evighet vil jeg bryte min pakt med eder;
2 ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
men I skal ikke gjøre pakt med dette lands innbyggere; deres altere skal I rive ned. Men I hørte ikke på mine ord; hvad har I gjort!
3 Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
Jeg sa også: Jeg vil ikke drive dem ut for eder, men de skal bli til brodder i eders sider, og deres guder skal bli til en snare for eder.
4 Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
Og da Herrens engel talte disse ord til alle Israels barn, gråt folket høit.
5 sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
Derfor kalte de dette sted Bokim, og de ofret der til Herren.
6 Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
Da Josva hadde latt folket fare, og Israels barn hadde draget hver til sin arv for å ta landet i eie,
7 Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
tjente folket Herren så lenge Josva levde, og så lenge alle de eldste levde som overlevde Josva og hadde sett alle de store gjerninger Herren hadde gjort for Israel.
8 Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
Men da Josva, Nuns sønn, Herrens tjener, var død, hundre og ti år gammel,
9 Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
og de hadde begravet ham på hans arvelodds grunn i Timnat-Heres i Efra'im-fjellene, nordenfor Ga'as-fjellet,
10 Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
og da hele denne slekt var samlet til sine fedre, og det efter dem var vokset op en annen slekt, som ikke kjente Herren, og heller ikke de gjerninger han hadde gjort for Israel,
11 Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
da gjorde Israels barn det som var ondt i Herrens øine, og dyrket Ba'alene.
12 Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
De forlot Herren, sine fedres Gud, som hadde ført dem ut av Egyptens land, og de fulgte andre guder av de folks guder som bodde rundt omkring dem, og de tilbad dem og vakte Herrens harme.
13 domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
De forlot Herren og dyrket Ba'al og Astarte-billedene.
14 Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
Da optendtes Herrens vrede mot Israel, og han gav dem i røveres hånd, som plyndret dem; han solgte dem i deres fienders hånd, de som bodde rundt omkring dem, og de kunde ikke mere stå sig mot sine fiender.
15 Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
Overalt hvor de drog ut, var Herrens hånd imot dem, så det gikk dem ille, således som Herren hadde sagt dem, og som Herren hadde svoret, og deres trengsel var stor.
16 Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
Da opreiste Herren dommere, og de frelste dem av røvernes hånd.
17 Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
Men heller ikke mot sine dommere var de lydige; de holdt sig med andre guder og tilbad dem; de vek snart av fra den vei deres fedre hadde vandret i lydighet mot Herrens bud, og gjorde ikke som de.
18 Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
Og når Herren opreiste dem dommere, så var Herren med dommeren og frelste dem av deres fienders hånd så lenge dommeren levde; for Herren ynkedes over dem når de sukket for deres skyld som plaget og undertrykte dem.
19 Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
Men når så dommeren døde, falt de igjen tilbake og fór verre frem enn sine fedre: De fulgte andre guder og dyrket dem og tilbad dem; de avstod ikke fra nogen av sine gjerninger eller fra sin gjenstridige ferd.
20 Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
Så optendtes Herrens vrede mot Israel, og han sa: Fordi dette folk har brutt min pakt, som jeg oprettet med deres fedre, og ikke har hørt på min røst,
21 ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
så vil jeg heller ikke mere drive bort for dem noget av de folk som Josva lot tilbake da han døde.
22 Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
Ved dem skulde Israel prøves, om de vilde ta vare på Herrens vei og vandre på den, som deres fedre gjorde, eller ikke.
23 Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.
Så lot da Herren disse folk bli og hastet ikke med å drive dem bort; han gav dem ikke i Josvas hånd.