< Mahukunta 2 >

1 Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
Or l'Ange de l'Eternel monta de Guilgal à Bokim, et dit: Je vous ai fait monter hors d'Egypte, et je vous ai fait entrer au pays dont j'avais juré à vos pères, et j'ai dit: Je n'enfreindrai jamais mon alliance que j'ai traitée avec vous.
2 ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
Et vous aussi vous ne traiterez point alliance avec les habitants de ce pays; vous démolirez leurs autels; mais vous n'avez point obéi à ma voix; qu'est-ce que vous avez fait?
3 Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
Et j'ai dit aussi: Je ne les chasserai point de devant vous, mais ils seront à vos côtés, et leurs dieux vous seront en piège.
4 Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
Et il arriva qu'aussitôt que l'Ange de l'Eternel eut dit ces paroles à tous les enfants d'Israël, le peuple éleva sa voix, et pleura.
5 sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
C'est pourquoi ils appelèrent ce lieu-là Bokim; et ils sacrifièrent là à l'Eternel.
6 Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
Or Josué avait renvoyé le peuple, et les enfants d'Israël s'en étaient allés chacun à son héritage, pour posséder le pays.
7 Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
Et le peuple avait servi l'Eternel tout le temps de Josué, et tout le temps des Anciens qui avaient survécu à Josué, [et] qui avaient vu toutes les grandes œuvres de l'Eternel, lesquelles il avait faites pour Israël.
8 Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
Puis Josué, fils de Nun, serviteur de l'Eternel, était mort, âgé de cent dix ans.
9 Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
Et on l'avait enseveli dans les bornes de son héritage à Timnath-Hérés, en la montagne d'Ephraïm, du côté du Septentrion de la montagne de Gahas.
10 Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
Et toute cette génération aussi avait été recueillie avec ses pères; puis une autre génération s'était levée après eux, laquelle n'avait point connu l'Eternel, ni les œuvres qu'il avait faites pour Israël.
11 Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
Les enfants d'Israël donc firent ce qui déplaît à l'Eternel, et servirent les Bahalins.
12 Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
Et ayant abandonné l'Eternel, le Dieu de leurs pères, qui les avait fait sortir du pays d'Egypte, ils allèrent après d'autres dieux, d'entre les dieux des peuples qui [étaient] autour d'eux, et ils se prosternèrent devant eux; ainsi ils irritèrent l'Eternel.
13 domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
Ils abandonnèrent donc l'Eternel, et servirent Bahal et Hastaroth.
14 Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
Et la colère de l'Eternel s'enflamma contre Israël, et il les livra entre les mains de gens qui les pillèrent; et il les vendit en la main de leurs ennemis d'alentour, de sorte qu'ils ne purent plus se maintenir devant leurs ennemis.
15 Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
Partout où ils allaient, la main de l'Eternel était contr'eux en mal, comme l'Eternel en avait parlé, et comme l'Eternel le leur avait juré, et ils furent dans de [grandes] angoisses.
16 Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
Et l'Eternel leur suscitait des Juges, qui les délivraient de la main de ceux qui les pillaient.
17 Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
Mais ils ne voulaient pas même écouter leurs Juges, ils paillardaient après d'autres dieux; ils se prosternaient devant eux; ils se détournaient aussitôt du chemin par lequel leurs pères avaient marché, obéissant aux commandements de l'Eternel; mais eux ne faisaient pas ainsi.
18 Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
Or quand l'Eternel leur suscitait des Juges, l'Eternel était aussi avec le Juge, et il les délivrait de la main de leurs ennemis pendant tout le temps du Juge; car l'Eternel se repentait pour les sanglots qu'ils jetaient à cause de ceux qui les opprimaient et qui les accablaient.
19 Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
Puis il arrivait que quand le Juge mourait, ils se corrompaient de nouveau plus que leurs pères, allant après d'autres dieux pour les servir, et se prosterner devant eux; ils ne diminuaient rien de leur mauvaise conduite ni de leur train obstiné.
20 Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
C'est pourquoi la colère de l'Eternel s'enflamma contre Israël, et il dit: Parce que cette nation a transgressé mon alliance que j'avais commandée à leurs pères, et qu'ils n ont point obéi à ma voix;
21 ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
Aussi je ne déposséderai plus de devant eux aucune des nations que Josué laissa quand il mourut;
22 Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
Afin d'éprouver par elles Israël, [et voir] s'ils garderont la voie de l'Eternel pour y marcher, comme leurs pères l'ont gardée, ou non.
23 Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.
L'Eternel donc laissa ces nations-là sans les déposséder sitôt, et il ne les livra point entre les mains de Josué.

< Mahukunta 2 >