< Mahukunta 2 >

1 Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
En ce temps-là, un ange du Seigneur vint de Galgala vers le Champ des Pleurs, vers Béthel et vers la maison de Joseph, à qui il dit: Voici ce que dit le Seigneur: Je vous ai fait sortir d'Egypte, je vous ai conduits en la terre que j'ai promise à vos pères, et j'ai dit: Je ne romprai pas l'alliance perpétuelle que j'ai faite avec vous.
2 ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
Et vous, vous ne ferez point alliance avec les peuples de cette terre, vous n'adorerez point leurs dieux, mais vous en briserez les images, et vous démolirez leurs autels. Or, vous avez été indociles à ma voix: car vous avez fait ce qui vous était défendu.
3 Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
Et j'ai dit: Je n'exterminerai point ces peuples devant votre face, et ils seront pour vous un sujet d'angoisse, et leurs dieux vous seront un objet de scandale.
4 Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
Lorsque l'ange du Seigneur eut dit ces paroles à tous les fils d'Israël, le peuple éleva la voix et pleura.
5 sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
Ils donnèrent à ce lieu le nom de Champ des Pleurs, et ils y sacrifièrent au Seigneur Dieu.
6 Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
Or, lorsque Josué avait congédié le peuple, chacun était allé prendre possession de son héritage.
7 Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
Et le peuple avait servi le Seigneur durant tous les jours de Josué et durant tous les jours des anciens, dont la vie s'était prolongée avec la sienne, et qui avaient vu toutes les œuvres du Seigneur en faveur d'Israël
8 Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
Et Josué, fils de Nau, serviteur de Dieu, était mort âgé de cent dix ans.
9 Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
Et on l'avait enseveli sur les limites de son héritage en Thamnatharès, dans les montagnes d'Ephraïm au nord des montagnes de Gaas,
10 Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
Toute cette génération s'était réunie à ses pères; et il s'éleva après elle une autre génération qui ne connaissait point le Seigneur, ni les œuvres du Seigneur en faveur d'Israël.
11 Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
Les fils d'Israël alors firent le mal devant le Seigneur, et ils servirent les Baal.
12 Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
Ils abandonnèrent le Seigneur Dieu de leurs pères qui les avait fait sortir de l'Egypte, et ils suivirent d'autres dieux parmi les dieux des nations qui les entouraient; ils les adorèrent, et ils excitèrent le courroux du Seigneur.
13 domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
Ils l'abandonnèrent, et ils servirent Baal et les Astartés.
14 Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
Alors le Seigneur fut courroucé contre Israël; il les livra aux mains de pillards qui les dépouillèrent; il les fit retomber entre les mains de leurs ennemis tout alentour, et ils ne purent résister devant leurs ennemis,
15 Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
De quelque côté qu'ils marchassent. Et la main du Seigneur était sur eux pour leur mal, comme l'avait dit le Seigneur Dieu, comme il le leur avait jurés, et il les affligea beaucoup.
16 Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
Ensuite, le Seigneur suscita des juges, et le Seigneur sauva le peuple des mains de ceux qui en faisaient leur proie.
17 Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
Et le peuple n'obéit pas aux juges, parce qu'il s'était prostituée à la suite des dieux étrangers, et qu'il les avait adorés; il dévia rapidement des voies ou avaient marché ses pères; il cessa d'écouter comme eux la parole du Seigneur.
18 Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
Et lorsque le Seigneur avait suscité des juges pour les fils d'Israël, et que le Seigneur était avec le juge, il les sauvait des mains de leurs ennemis, durant tous les jours du juge, parce que le Seigneur était ému de leurs gémissements devant ceux qui les assiégeaient et les affligeaient.
19 Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
Mais, lorsque le juge était mort, ils changeaient et retombaient dans une corruption plus grande que celle de leurs pères, en suivant d'autres dieux, en les servant et en les adorant. Ils ne pouvaient alors renoncer à leurs habitudes ni à leurs voies d'endurcissement.
20 Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
Le Seigneur se courrouça donc contre Israël, et il dit: Pour punir ce peuple d'avoir abandonné l'alliance que j'avais faite avec ses pères, et de n'avoir pas écouté ma parole,
21 ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
Je ne ferai plus périr un seul homme de ceux qu'a laissés en cette terre Josué, fils de Nau, et qu'a laissés le Seigneur,
22 Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
Pour éprouver par eux Israël, et voir s'il persévèrerait ou non dans la voie du Seigneur qu'avaient suivie leurs pères.
23 Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.
Et le Seigneur permettra encore que les nations qu'il n'a pas livrées aux mains de Josué, ne soient point exterminées rapidement.

< Mahukunta 2 >