< Mahukunta 2 >
1 Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
Un envoyé du Seigneur s’en vint de Ghilgal à Bokhîm et dit de sa part: "Je vous avais fait monter d’Egypte et entrer dans le pays que j’avais promis par serment à vos pères, et j’avais dit: "Je ne romprai jamais mon alliance avec vous;
2 ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
mais à votre tour ne transigez point avec les habitants de ce pays, détruisez leurs autels!" Et vous n’avez pas écouté ma voix. Qu’avez-vous fait là!
3 Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
Aussi ai-je résolu de ne pas les chasser de devant vous; et ils s’attacheront à vos flancs, et leurs divinités seront pour vous un écueil."
4 Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
Quand l’envoyé du Seigneur eut ainsi parlé à tous les enfants d’Israël, le peuple éclata en pleurs;
5 sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
on nomma cet endroit Bokhîm, et l’on y sacrifia à l’Eternel.
6 Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
Or, lorsque Josué eut congédié le peuple et que les enfants d’Israël, prenant possession du pays, s’installèrent chacun dans son héritage,
7 Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
le peuple servit l’Eternel pendant toute la vie de Josué, et tout le temps que vécurent, après lui, les vieillards témoins de toutes les grandes œuvres que Dieu avait accomplies pour Israël.
8 Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
Josué, fils de Noun, serviteur de l’Eternel, mourut à l’âge de cent dix ans.
9 Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
On l’ensevelit dans le territoire de sa possession, à Timnat-Hérès, dans la montagne d’Ephraïm, au nord du mont Gaach.
10 Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
Quand toute cette génération, à son tour, fut réunie à ses pères, une autre génération lui succéda, qui ne connaissait point l’Eternel, ni ce qu’il avait fait pour Israël.
11 Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
Les enfants d’Israël firent ce qui déplaît à l’Eternel, ils adorèrent les Bealim.
12 Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
Abandonnant l’Eternel, Dieu de leurs pères, qui les avait tirés du pays d’Egypte, ils s’attachèrent à d’autres dieux, choisis parmi ceux des peuples d’alentour, se prosternèrent devant eux et irritèrent l’Eternel.
13 domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
Ils abandonnèrent ainsi l’Eternel, pour servir Baal et les Astarot.
14 Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
Alors la colère de l’Eternel s’alluma contre Israël, il les abandonna aux déprédations de peuples pillards, les livra aux ennemis qui les entouraient, et ils ne furent plus capables de leur tenir tête.
15 Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
Dans toutes leurs expéditions, la main de l’Eternel intervenait à leur désavantage, comme il l’avait annoncé, comme il le leur avait juré; ils furent ainsi réduits à la plus grande détresse.
16 Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
Alors Dieu suscita des juges, qui les délivrèrent de la main de leurs déprédateurs.
17 Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
Mais ils n’obéirent pas non plus à leurs juges: loin de là, ils se prostituèrent à des dieux étrangers et se prosternèrent devant eux; promptement infidèles à la voie qu’avaient suivie leurs pères, ils n’écoutèrent pas, comme eux, les commandements du Seigneur.
18 Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
Quand l’Eternel leur suscitait des juges, il assistait ceux-ci et délivrait les Israélites du pouvoir de leurs ennemis tant que vivait le juge; car l’Eternel se laissait fléchir par leurs gémissements que provoquaient leurs oppresseurs et leurs tyrans.
19 Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
Puis, le juge mort, ils recommençaient à agir plus mal encore que leur ancêtres en s’attachant à des dieux étrangers, en les servant et en se prosternant devant eux, en ne renonçant enfin ni à leurs méfaits, ni à leur conduite déréglée.
20 Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
Aussi l’Eternel s’irrita contre Israël et dit: "Puisque cette nation a transgressé le pacte que j’avais imposé à ses pères, puisqu’ils n’ont pas écouté ma voix,
21 ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
à mon tour, je ne veux plus déposséder, en leur faveur, aucun des peuples que Josué a laissé subsister lorsqu’il est mort.
22 Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
Ils me serviront à éprouver les Israélites, à juger s’ils s’appliquent ou non à suivre les voies de l’Eternel comme l’on fait leurs ancêtres."
23 Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.
L’Eternel s’abstint donc de hâter la dépossession de ces peuples, de même qu’il ne les avait point livrés au pouvoir de Josué.