< Mahukunta 2 >

1 Mala’ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim ya ce, “Na hauro da ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba wa kakanninku. Na ce, ‘Ba zan taɓa tā da yarjejjeniyata da ku ba,
Anđeo Jahvin dođe iz Gilgala u Bokim i reče: “Izveo sam vas iz Egipta i doveo vas u zemlju koju sam vam obećao zaklevši se ocima vašim. Rekao sam: 'Neću raskinuti Saveza svog s vama dovijeka.
2 ku kuma kada ku shiga wata yarjejjeniya da mazaunan ƙasan nan, sai dai za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya mini ba. Me ya sa kuka yi haka?
A vi ne sklapajte saveza sa stanovnicima ove zemlje; nego rušite njihove žrtvenike!' Ali vi niste poslušali moga glasa. Što ste učinili?
3 Saboda haka ina gaya muku cewa ba zan kore su a gabanku ba; za su zama muku ƙaya, gumakansu kuma za su zama muku tarko.”
Zato vam kažem: neću ih odagnati pred vama. Nego, oni će vas tlačiti i bogovi njihovi bit će vam zamkom.”
4 Da mala’ikan Ubangiji ya faɗa wa dukan Isra’ilawa waɗannan abubuwa, sai mutane suka yi kuka mai zafi,
Kad Anđeo Jahvin izreče te riječi svim Izraelcima, narod zakuka i zaplaka.
5 sai suka sa wa wannan wuri suna, Bokim. A nan suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji.
I tako prozvaše ono mjesto Bokim i ondje prinesoše žrtve Jahvi.
6 Bayan Yoshuwa ya sallami Isra’ilawa, sai suka tafi don su mallaki ƙasar, kowa da nasa gādon.
Tada Jošua otpusti narod i raziđoše se Izraelci svaki na svoju baštinu da zaposjednu zemlju.
7 Mutane suka bauta wa Ubangiji duk tsawon kwanakin Yoshuwa da na dattawan da suka rayu bayansa waɗanda suka ga manyan abubuwan da Ubangiji ya yi wa Isra’ila.
Narod je služio Jahvi svega vijeka Jošuina i svega vijeka starješina koje su nadživjele Jošuu i vidjele sva velika djela što ih je Jahve učinio Izraelu.
8 Yoshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya mutu yana da shekara ɗari da goma.
Jošua, sin Nunov, sluga Jahvin, umrije u dobi od sto deset godina.
9 Aka binne shi a ƙasar gādonsa, a Timnat Heres a ƙasar tudu ta Efraim, arewa da Dutsen Ga’ash.
Sahraniše ga u kraju što ga je baštinio u Timnat Heresu, u Efrajimovoj gori, sjeverno od planine Gaaša.
10 Bayan tsaran nan duka suka rasu, sai wata tsara ta taso wadda ba tă san Ubangiji ko abin da ya yi wa Isra’ila ba.
A kada se sav onaj naraštaj pridružio svojim ocima, naslijedi ga drugi naraštaj koji nije mario za Jahvu ni za djela što ih je učinio Izraelu.
11 Sai Isra’ilawa suka yi mugaye abubuwa a gaban Ubangiji suka kuma bauta Ba’al.
Tada su sinovi Izraelovi počeli činiti ono što Jahvi nije po volji i služili su baalima.
12 Suka yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar. Suka bi suka kuma bauta alloli dabam-dabam na mutanen da suke kewaye da su. Suka tsokani Ubangiji ya yi fushi
Ostaviše Jahvu, Boga otaca svojih, koji ih je izveo iz zemlje egipatske, i pođoše za drugim bogovima između bogova okolnih naroda. Klanjahu im se, razgnjeviše Jahvu.
13 domin sun bar shi suka bauta wa Ba’al da Ashtarot.
Otpali su od Jahve da bi služili Baalu i Aštarti.
14 Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
Zato Jahve izli gnjev svoj na Izraela: prepusti ih pljačkašima da ih plijene, izruči ih neprijateljima uokolo, tako te se ne mogoše oduprijeti.
15 Duk sa’ad da Isra’ila suka fita yaƙi, Ubangiji yakan yi gāba da su don a ci su a yaƙi, kamar dai yadda ya rantse musu. Suka kuwa shiga wahala ƙwarai.
Što bi god počeli, ruka se Jahvina okretala protiv njih na njihovu nesreću, kao što im je Jahve rekao i kao što im se zakleo. I tako zapadoše u veliku nevolju.
16 Sa’an nan Ubangiji ya naɗa mahukunta, waɗanda suka cece su daga hannun waɗannan musu hari.
Tada im Jahve stade podizati suce da ih izbavljaju iz ruku onih koji su ih pljačkali.
17 Duk da haka ba su saurari mahukuntansu ba amma sai suka shiga ha’inci da waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Ba kamar kakanninsu ba, nan da nan suka kauce daga hanyar da kakanninsu suka bi, hanyar biyayya ga umarnan Ubangiji.
Ali oni ni svojih sudaca nisu slušali, nego se iznevjeriše s drugim bogovima te im se klanjahu. Brzo su zašli s puta kojim su išli oci njihovi slušajući Jahvine zapovijedi; oni nisu činili tako.
18 Duk sa’ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan kasance tare da mahukuncin, yă kuma cece su daga hannun abokan gāba, muddin mahukuncin yana a raye; gama Ubangiji yakan ji tausayinsu yayinda suke gunaguni ƙarƙashin waɗanda suka danne su suke kuma gasa musu azaba.
Kada im je podizao suce, Jahve bijaše sa svakim sucem te ih izbavljaše iz ruku njihovih neprijatelja za svega vijeka sučeva, jer se sažalilo Jahvi koliko su uzdisali pod jarmom onih koji su ih ugnjetavali.
19 Amma sa’ad da mahukuncin ya mutu, mutanen suka koma hanyar da ta fi ta kakanninsu muni, sukan bi waɗansu alloli suna bauta musu. Suka ƙi barin mugun ayyukansu da taurin zuciyarsu.
A kada bi sudac umro, oni bi opet zapadali u veću pokvarenost nego njihovi oci. Išli su za drugim bogovima, služili im i klanjali im se, ne odustajući od svojih opakih djela i postupaka.
20 Saboda haka sai Ubangiji ya fusata da Isra’ila ya ce, “Domin wannan al’umma ta tā da yarjejjeniyar da na yi da kakanninsu ba su kuwa saurare ni ba,
Tada Jahve planu gnjevom na Izraela i reče: “Kad je taj narod pogazio Savez kojim sam obvezao njihove očeve i nije poslušao glasa moga,
21 ba zan ƙara kori wata al’ummar da Yoshuwa ya bari sa’ad da ya rasu ba.
ni ja odsad neću pred njim potjerati ni jednoga između naroda što ih je Jošua po svojoj smrti ostavio”,
22 Zan yi amfani da su in gwada Isra’ila in ga ko za su bi hanyar Ubangiji su kuma yi tafiya a cikinta kamar yadda kakanninsu suka yi.”
da bi njima stavio na kušnju Izraela: hoće li se ili neće držati Jahvinih putova kao što ih se držahu oci njihovi.
23 Ubangiji ya bar waɗannan al’ummai su kasance; bai kore su nan take ta wurin ba da su a hannun Yoshuwa ba.
Zato Jahve bijaše ostavio te narode i nije ih odmah izagnao ni predao Jošui u ruke.

< Mahukunta 2 >