< Mahukunta 19 >

1 A kwanakin nan Isra’ila ba su da sarki. To, wani Balawe wanda yake zama a wani lungu na ƙasar tudu ta Efraim ya ɗauko wa kansa ƙwarƙwara daga Betlehem cikin Yahuda.
At that time the Israeli people had no king. There was a man from the tribe of Levi who lived in a remote place in the hilly area where the tribe of Ephraim lives. He had previously taken as a wife a woman who was a slave. She was from Bethlehem, in the area where the tribe of Judah lives.
2 Amma ba tă yi aminci ba. Ta bar shi ta komo gidan mahaifiyarta a Betlehem, a Yahuda. Bayan ta zauna a can wajen wata huɗu,
But she started to sleep with other men also. Then she left him and returned to her father’s house in Bethlehem. She stayed there for four months.
3 sai mijinta ya je wajenta biko don yă rarashe ta komo. Ya tafi tare bawansa da kuma jakuna biyu. Sai ta shigar da shi gidan mahaifinta, sa’ad da mahaifinta ya gan shi, ya marabce shi da murna.
Then her husband took his servant and two donkeys and went to Bethlehem. He went to ask her to come back to live with him again. When he arrived at her father’s house, she invited him to come in. Her father was happy to see him.
4 Surukinsa, mahaifin yarinyar, ya sha kansa, yă dakata; saboda haka ya dakata tare da shi har kwana uku, yana ci yana sha, yana kuma kwanciya a can.
The woman’s father asked him to stay. So he stayed there for three days. During that time he ate and drank and slept there.
5 A rana ta huɗu suka tashi da sassafe ya kuma yi shiri yă tafi, amma mahaifinta yarinyar ya ce wa surukinsa, “Ka ɗan ci wani abu don ka sami ƙarfi; sa’an nan ka tafi.”
On the fourth day, they all got up early in the morning. The man from the tribe of Levi was preparing to leave, but the woman’s father said to him, “Eat something before you go.”
6 Saboda haka suka zauna su biyu suka ci suka sha tare. Bayan haka sai mahaifin yarinyar ya ce, “Don Allah ka kwana ka ji wa kanka daɗi.”
So the two men sat down to eat and drink together. Then the woman’s father said to him, “Please stay another night. Relax/Rest and have a joyful time.”
7 Sa’ad da mutumin ya tashi zai tafi, sai surukinsa ya roƙe shi, saboda haka ya kwana a wannan dare.
The man from the tribe of Levi wanted to leave, but the woman’s father requested him to stay one more night. So he stayed again that night.
8 Da sassafen kashegari rana ta biyar, ya tashi zai tafi, sai mahaifin yarinyar ya ce, “Ka ɗan zauna ka shaƙata sai rana ta yi sanyi mana!” Saboda haka su biyu suka zauna suka ci abinci tare.
On the fifth day, the man got up early and prepared to leave. But the woman’s father said to him again, “Have something to eat. Wait until this afternoon, [and then leave].” So the two men ate together.
9 Sa’ad da mutumin da ƙwarƙwaransa da bawansa, suka tashi don su tafi, surukinsa, mahaifin yarinyar ya ce, “Duba, rana ta kusan fāɗuwa, yamma ta riga ta yi, ka kwana a nan. Ka sāke kwana ka ji wa ranka daɗi. Kashegari da sassafe za ka iya tashi ka kama hanyarka zuwa gida.”
In the afternoon, when the man from the tribe of Levi and his slave wife and his servant got up to leave, the woman’s father said, “It will soon be dark. The day is almost over. Stay here tonight and have a good/joyful time. Tomorrow morning you can get up early and leave for your home.”
10 Amma bai so ya sāke kwana a can ba, mutumin ya tashi ya tafi ya bi ta Yebus (wato, Urushalima), tare da jakunansa biyu da aka yi musu shimfiɗa da kuma ƙwarƙwaransa.
But the man from the tribe of Levi did not want to stay for another night. He put saddles on his two donkeys, and started to go with his slave wife [and his servant] toward Jebus [city], which is [now named] Jerusalem.
11 Sa’ad da suka yi kusa da Yebus dare kuma ya riga ya yi, bawan ya ce wa maigidansa, “Mu dakata a birnin nan na Yebusiyawa mu kwana.”
Late in the afternoon, they came near to Jebus. The servant said to his master, “We should stop in this city where the Jebus people-group live, and stay here tonight.”
12 Maigidansa ya ce, “A’a. Ba za mu shiga birnin baƙi waɗanda mutanensu ba Isra’ilawa ba. Za mu ci gaba zuwa Gibeya.”
But his master said, “No, it would not be good for us to stay here where foreign people live. There are no Israeli people here. We will go on to Gibeah [city].”
13 Ya kuma ce, “Zo, mu yi ƙoƙari mu kai Gibeya ko Rama mu kwana a ɗaya cikinsu.”
He said to his servant, “Let’s go. It is not far to Gibeah. We can go there, or we can go a bit further to Ramah. We can stay in one of those two cities tonight.”
14 Saboda haka suka ci gaba, rana tana fāɗuwa sa’ad da suka yi kusa da Gibeya a Benyamin.
So they continued walking. When they came near Gibeah, where people from the tribe of Benjamin live, the sun was setting.
15 A can suka dakata don su kwana, suka tafi suka zauna a dandali birnin, amma wani ya shigar da su gidansa da daren.
They stopped to stay there that night. They went to the public square of that city and sat down. But no one [who passed by] invited them to stay in their house for that night.
16 A wannan yamma sai ga wani tsoho daga ƙasar tudu ta Efraim, wanda yake zama a Gibeya (mutane wurin kuwa mutanen Benyamin ne), ya shigo daga wurin aiki a gonaki.
Finally, in the evening, an old man came by. He had been working in the fields. He was from the hilly area of the tribe of Ephraim, but at that time he was living in Gibeah.
17 Sa’ad da ya duba ya ga matafiyin a dandalin birnin, sai tsohon ya yi tambaya ya ce, “Ina za ku? Ina kuka fito?”
He realized that the man from the tribe of Levi was only traveling and did not have a home in that city. So he asked the man, “Where have you come from? And where are you going?”
18 Balawen ya ce, “Muna fito daga Betlehem a Yahuda za mu wani lungu a ƙasar tudu ta Efraim inda nake da zama. Na tafi Betlehem a Yahuda, ga shi kuwa yanzu za ni gidan Ubangiji. Ba wanda ya shigar da ni gidansa.
He replied, “We are traveling from Bethlehem to my home in the hilly area where people of the tribe of Ephraim live. I went from there to Bethlehem, but now we are going to [Shiloh] where Yahweh’s Sacred tent (OR, my house) is. No one here has invited us to stay in their house tonight.
19 Muna da ƙara da abinci don jakunanmu, muna kuma da burodi da ruwan inabi dominmu da bayinka, ni, baiwarka da kuma saurayin nan tare da mu. Ba ma bukatar kome.”
We have straw and food for our donkeys, and bread and wine for me and the young woman and my servant. We do not need anything else.”
20 Tsohon ya ce, “Na marabce ku a gidana. Bari ni ba ku duk abin da kuke bukata. Kada ku dai kwana a dandali.”
The old man said, “I wish that things will go well for you, but I would like to provide what you need. Do not stay here in the square tonight.”
21 Saboda haka sai kai shi zuwa gidansa ya ciyar da jakunansa. Bayan sun wanke ƙafafunsu, sai aka ba su abinci da abin sha.
Then the old man took them to his house. He gave food to the donkeys. He [gave water to the man and the woman and the servant to] wash their feet. And he gave them something to eat and drink.
22 Yayinda suke jin wa kansu daɗi, sai waɗansu’yan iska daga birnin suka kewaye gidan. Suna bubbuga ƙofar, suna kira tsohon da yake da gidan suna cewa, “Ka fito mana da mutumin nan a gidanka domin mu yi jima’i da shi.”
While they were having a good/joyful time together, some wicked men from that city surrounded the house and started to bang on the door. They shouted to the old man, “Bring out to us the man who has come to your house. We want to have sex with him.”
23 Maigidan ya fita waje ya ce musu, “A’a, abokaina, kada ku yi abin kunyan nan. Da yake mutumin nan baƙona ne, kada ku yi rashin kunyan nan.
The old man went outside and said to them, “Friends, I will not do that. That would be a very evil thing. This man is a guest in my house. You should not do such a terrible/disgraceful/shameful thing!
24 Duba, ga’yata da ba tă taɓa sanin namiji ba da kuma ƙwarƙwaransa. Zan fito muku da su a waje yanzu, za ku kuwa iya yin ko mene ne da kuke so da su. Amma wannan mutum, kada ku yi abin kunya.”
Look, my daughter is here. She is [still] a virgin. And this man’s slave wife is here. I will bring them out to you now. You may do to them whatever you wish, but do not do such a terrible/disgraceful/shameful thing to this young man!”
25 Amma mutanen ba su saurare shi ba. Saboda haka mutumin ya ba da ƙwarƙwaransa, suka yi mata fyaɗe suka yi lalata da ita dukan dare, gari yana wayewa sai suka bar ta.
But the men did not pay attention to what he said. So the man from the tribe of Levi took his slave wife and sent her to them, outside the house. They raped [EUP] her and abused her all night. Then at dawn, they allowed her to go.
26 Da safe matar ta koma gidan da maigidanta yake, ta fāɗi a ƙofa ta kwanta a can har rana ta yi.
She returned to the old man’s house, where her husband was staying, but she fell down at the doorway and lay there all night.
27 Sa’ad da maigidanta ya tashi da safe ya buɗe ƙofar gidan don yă fita ya ci gaba da tafiyarsa, sai ga ƙwarƙwararsa, ta fāɗi a bakin ƙofar gidan da hannuwanta a madogarar ƙofar.
In the morning, when the man from the tribe of Levi got up, he went outside of the house to continue his journey. He saw his slave wife lying there at the doorway of the house. Her hands were on the doorsill.
28 Ya ce mata, “Tashi; mu tafi.” Amma ba amsa. Sai ya sa ta a kan jakinsa ya kama hanyar gida.
He said to her, “Get up! Let’s go!” But she did not answer, [because she had died]. He put her body on the donkey and traveled to his home.
29 Da ya kai gida, sai ya ɗauki wuƙa ya yayyanka ƙwarƙwaransa gunduwa-gunduwa, kashi goma sha biyu ya aika da su a ko’ina a Isra’ila.
When he arrived home, he took a knife and cut the body of the slave woman into twelve pieces. Then he sent one piece to each area of Israel, [along with a message telling what had happened].
30 Duk wanda ya gani, sai ya ce, “Ba a taɓa gani ko yin irin wannan abu ba, tun lokacin da Isra’ilawa suka fito daga Masar. Ku yi tunani wannan! Ku kuma yi la’akari! Ku gaya mana abin da za mu yi!”
Everyone who saw a piece of the body and the message said, “Nothing like this has ever happened before. Not since our ancestors left Egypt [have we heard of such a terrible thing]. We need to think carefully about it. Someone should decide what we should do.”

< Mahukunta 19 >