< Mahukunta 17 >

1 To, wani mutum mai suna Mika daga ƙasar tudu ta Efraim
Or il y avait un homme de la montagne d'Ephraïm, duquel le nom était Mica;
2 ya ce wa mahaifiyarsa, “Shekel dubu ɗaya da ɗari ɗaya na azurfa da aka ɗauka daga gare ki wanda kuma ji kin furta la’ana a kai, azurfan yana wurina; ni ne na ɗauka.” Sa’an nan mahaifiyarsa ta ce, “Ubangiji yă albarkace ka ɗana!”
Qui dit à sa mère: Les onze cents [pièces] d'argent qui te furent prises, pour lesquelles tu fis des imprécations, en ma présence, voici, j'ai cet argent-là par-devers moi; je l'avais pris. Alors sa mère dit: Béni soit mon fils par l'Eternel.
3 Sa’ad da ya mayar da azurfa dubu ɗaya da ɗari ɗaya na shekel wa mahaifiyarsa, sai ta ce, “Na ba da azurfata ga Ubangiji don ɗana yă sassaƙa sura yă kuma yi zubin gunki. Zan mayar maka.”
Et quand il rendit à sa mère les onze cents [pièces] d'argent, sa mère dit: J'avais entièrement dédié de ma main cet argent à l'Eternel pour mon fils, afin d'en faire une image taillée, et une de fonte, ainsi je te le rendrai maintenant.
4 Saboda haka ya mayar da azurfan wa mahaifiyarsa, ita kuwa ta ɗauki azurfa ɗari biyu na shekel ta ba wa maƙeri, wanda ya mai da su sura da kuma gunki. Aka kuwa sa su a gidan Mika.
Après donc qu'il eut rendu cet argent à sa mère, elle en prit deux cents [pièces], et les donna au fondeur, qui en fit une image taillée, et une de fonte; et elles furent dans la maison de Mica.
5 To, wannan mutum Mika yana da ɗakin gumaka, ya yi efod da waɗansu gumaka, ya kuma naɗa ɗaya daga cikin’ya’yansa firist nasa.
Ainsi cet homme, [savoir] Mica, eut une maison de dieux, et fit un Ephod et des Théraphims, et consacra l'un de ses fils, qui lui servit de Sacrificateur.
6 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa yana yin abin da ya ga dama.
En ce temps-là il n'y avait point de Roi en Israël; chacun faisait ce qui lui semblait être droit.
7 Wani saurayi Balawe daga Betlehem a Yahuda, wanda yake zama cikin zuriyar Yahuda,
Or il y eut un jeune homme de Bethléhem de Juda, [ville] de la famille de Juda, qui était Lévite, et qui avait fait là son séjour;
8 ya bar garin ya tafi neman inda zai zauna. A hanyarsa ya zo gidan Mika a ƙasar tudu ta Efraim.
Lequel partit de cette ville-là, [savoir] de Bethléhem de Juda, pour aller demeurer où il trouverait [sa commodité], et continuant son chemin, il vint en la montagne d'Ephraïm jusqu'à la maison de Mica.
9 Mika ya ce masa, “Daga ina kake?” Ya ce, “Ni Balawe ne daga Betlehem a Yahuda, ina kuwa neman wurin zauna ne.”
Et Mica lui dit: D'où viens-tu? Le Lévite lui répondit: Je suis de Bethléhem de Juda, et je m'en vais pour demeurer où je trouverai [ma commodité].
10 Sa’an nan Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni ka zama mini mahaifi da firist, zan kuwa ba ka azurfa goma na shekel a shekara, tufafinka da kuma abincinka.” Sai Balawen ya tafi.
Et Mica lui dit: Demeure avec moi, et sois-moi pour père et pour Sacrificateur, et je te donnerai dix [pièces] d'argent par an, et ce que tes habits coûteront, et ta nourriture. Et le Lévite y alla.
11 Saboda haka Balawen ya yarda ya zauna tare da shi, ɗan saurayin kuwa ya zama kamar ɗaya daga cikin’ya’yansa.
Ainsi le Lévite convint de demeurer avec cet homme-là, et ce jeune homme lui fut comme l'un de ses enfants.
12 Sa’an nan Mika ya naɗa Balawen, saurayin kuwa ya zama masa firist ya kuma zauna a gidansa.
Et Mica consacra le Lévite, et ce jeune homme lui servit de Sacrificateur, et demeura en sa maison.
13 Mika ya ce, “Yanzu na san cewa Ubangiji zai yi mini alheri, da yake Balawen nan ya zama firist nawa.”
Alors Mica dit: Maintenant je connais que l'Eternel me fera du bien, parce que j'ai un Lévite pour Sacrificateur.

< Mahukunta 17 >