< Mahukunta 17 >
1 To, wani mutum mai suna Mika daga ƙasar tudu ta Efraim
Il y avait un homme de la montagne d’Ephraïm, nommé Michas.
2 ya ce wa mahaifiyarsa, “Shekel dubu ɗaya da ɗari ɗaya na azurfa da aka ɗauka daga gare ki wanda kuma ji kin furta la’ana a kai, azurfan yana wurina; ni ne na ɗauka.” Sa’an nan mahaifiyarsa ta ce, “Ubangiji yă albarkace ka ɗana!”
Il dit à sa mère: « Les mille et cent sicles d’argent qu’on t’a pris, et au sujet desquels tu as prononcé une malédiction, — et tu l’as même prononcée à mes oreilles, — voici, cet argent est entre mes mains, c’est moi qui l’ai pris. » Et sa mère dit: « Que mon fils soit béni de Yahweh! »
3 Sa’ad da ya mayar da azurfa dubu ɗaya da ɗari ɗaya na shekel wa mahaifiyarsa, sai ta ce, “Na ba da azurfata ga Ubangiji don ɗana yă sassaƙa sura yă kuma yi zubin gunki. Zan mayar maka.”
Il rendit à sa mère les mille et cent sicles d’argent; et sa mère dit: « Je consacre de ma main cet argent à Yahweh pour mon fils, afin d’en faire une image taillée et un objet en fonte; et maintenant je te le rends. »
4 Saboda haka ya mayar da azurfan wa mahaifiyarsa, ita kuwa ta ɗauki azurfa ɗari biyu na shekel ta ba wa maƙeri, wanda ya mai da su sura da kuma gunki. Aka kuwa sa su a gidan Mika.
Lorsqu’il eut rendu l’argent à sa mère, sa mère prit deux cents sicles et les donna au fondeur, qui en fit une image taillée et un objet en fonte; et ils furent dans la maison de Michas.
5 To, wannan mutum Mika yana da ɗakin gumaka, ya yi efod da waɗansu gumaka, ya kuma naɗa ɗaya daga cikin’ya’yansa firist nasa.
Car ce Michas avait une maison de Dieu; il fit un éphod et des théraphim, et il consacra un de ses fils, qui lui servit de prêtre.
6 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa yana yin abin da ya ga dama.
En ce temps-là, il n’y avait pas de roi en Israël; chacun faisait ce qui était bon à ses yeux.
7 Wani saurayi Balawe daga Betlehem a Yahuda, wanda yake zama cikin zuriyar Yahuda,
Il y avait un jeune homme de Bethléem de Juda, de la famille de Juda; il était Lévite et séjournait dans cette ville.
8 ya bar garin ya tafi neman inda zai zauna. A hanyarsa ya zo gidan Mika a ƙasar tudu ta Efraim.
Cet homme partit de la ville de Bethléem de Juda, pour trouver un lieu de séjour. Il arriva ainsi dans la montagne d’Éphraïm, jusqu’à la maison de Michas.
9 Mika ya ce masa, “Daga ina kake?” Ya ce, “Ni Balawe ne daga Betlehem a Yahuda, ina kuwa neman wurin zauna ne.”
Michas lui dit: « D’où viens-tu? » Il lui répondit: « Je suis Lévite, de Bethléem de Juda, et je voyage pour trouver un lieu de séjour. »
10 Sa’an nan Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni ka zama mini mahaifi da firist, zan kuwa ba ka azurfa goma na shekel a shekara, tufafinka da kuma abincinka.” Sai Balawen ya tafi.
Michas lui dit: « Reste avec moi; sois pour moi un père et un prêtre, et je te donnerai dix sicles d’argent par an, une provision de vêtements et la nourriture. » Et le Lévite entra.
11 Saboda haka Balawen ya yarda ya zauna tare da shi, ɗan saurayin kuwa ya zama kamar ɗaya daga cikin’ya’yansa.
Le Lévite consentit à demeurer chez cet homme, et le jeune homme fut pour lui comme l’un de ses fils.
12 Sa’an nan Mika ya naɗa Balawen, saurayin kuwa ya zama masa firist ya kuma zauna a gidansa.
Michas installa le Lévite, et le jeune homme lui servit de prêtre et demeura dans la maison de Michas.
13 Mika ya ce, “Yanzu na san cewa Ubangiji zai yi mini alheri, da yake Balawen nan ya zama firist nawa.”
Et Michas dit: « Je sais maintenant que Yahweh me fera du bien, puisque j’ai ce Lévite pour prêtre. »